Yan ta'addan ISWAP sun kaiwa Soji harin kwantan bauna, sun kashe jami'ai 19

Yan ta'addan ISWAP sun kaiwa Soji harin kwantan bauna, sun kashe jami'ai 19

Yan ta'adda ISWAP sun kai wa tawagar motocin rundunar Soji harin kwantan bauna a jihar Borno inda suka hallaka Soji 15 tare da yan banga hudu, majiyoyi sun bayyana ranar Asabar.

Yan ta'addan sun kai wannan hari ne kusa da Gudumbali a yankin tafkin Chadi ranar Alhamis, cewar majiyoyin.

Wani jami'in Soja wanda ya bukaci a sakaye sunansa ya bayyanawa AFP cewa "mun rasa Sojoji 15 da CJTF hudu a harin da yan ta'adda suka kai a dajin dake kusa da Gudumbali."

Ya kara da cewa akalla dakaru 13 sun jigara a harin.

Tawagar motocin Soji 10 na kan hanyar zuwa Gudumbali ne daga garin Kukawa don kaiwa yan ta'addan farmaki sai aka bude musu wuta, cewar wata majiya daban.

A ranar Asabar, kungiyar masu tada kayar bayan ISWAP sun dau alhakin wannan hari.

An kafa ISWAP ne bayan ballewar Boko Haram a 2016.

Yan ta'addan kungiyar sun shahara da kaiwa Sojoji hari mazauninsu tare da garkuwa da matafiya a kan hanya suna kashesu.

Yan ta'addan ISWAP sun kaiwa Soji harin kwantan bauna, sun kashe jami'ai 19
Yan ta'addan ISWAP sun kaiwa Soji harin kwantan bauna, sun kashe jami'ai 19
Asali: Depositphotos

Asali: Legit.ng

Online view pixel