Dumbin masu zanga-zangar ENDSARS sun dawo suna 'romon baka' akan aikin dan sanda

Dumbin masu zanga-zangar ENDSARS sun dawo suna 'romon baka' akan aikin dan sanda

- IGP Mohammed Adamu, babban sifeton rundunar 'yan sanda ya tona asirin wasu matasa da suka gudanar da zanga-zangar ENDSARS

- An gudanar da zangar-zangar ENDSARS ne a shekarar 2020 domin nuna adawa da zaluncin 'yan sanda da neman a rushe rundunar SARS

- Zangar-zangar, wacce aka fara a matsayin ta lumana, ta rikide zuwa kazamin rikici a jihohin da ta samu karbuwa a sassan Nigeria

Babban sifeton rundunar 'yan sandan Nigeria, IGP Mohammed Adamu, ya bayyana cewa akwai dumbin matasan da suka gudanar da zanga-zangar ENDSARS a cikin masu neman aikin dan sanda.

A cikin watan Oktobar shekarar 2020 ne aka fara gudanar da zanga-zangar ENDSARS ta nuna adawa da neman a rushe rundunar 'yan sandan SARS.

Zanga-zangar ENDSARS, wacce aka fara a matsayin ta lumana, ta rikide zuwa rikicin da ya yi sanadiyyar asarar rayuka da dukiya.

Da yake magana a gidan talabijin din Channels yayin wata hira da shi, IGP Adamu ya bayyana cewa wasu daga cikin matasan da suka gudanar da zanga-zangar suna daga cikin masu neman a daukesu aikin dan sanda.

Dumbin masu zanga-zangar ENDSARS sun dawo suna 'romon baka' akan aikin dan sanda
Dumbin masu zanga-zangar ENDSARS sun dawo suna 'romon baka' akan aikin dan sanda
Asali: Twitter

"Da dama daga cikinsu sun dawo suna neman aikin dan sanda, har roko suke yi a taimaka a daukesu aikin dan sanda tare da yin romon bakan cewa aikin Allah ne.

A kwanakin baya Legit.ng ta rawaito shugaban kasa, Muhammadu Buhari, na cewa ko kadan ba ya jin dadin yadda 'yan ta'adda ke salwantar da rayukan jama'a a sassan Nigeria

A cewar Buhari, gwamnatinsa ta yi wasu tsare-tsare domin kawo karshen kungiyar Boko haram a cikin shekarar 2021.

Buhari ya lissafa wasu jiga-jigan dalilai guda hudu da zasu bawa gwamnatinsa damar ganin bayan kungiyar Boko Haram da sauran kungiyoyin 'yan ta'adda a cikin wannan shekarar, 2021.

Don sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel