Ku kare kanku idan an kawo muku hari, IGP ya fada wa 'Yan sanda

Ku kare kanku idan an kawo muku hari, IGP ya fada wa 'Yan sanda

- Shugaban ƴan sandan Najeriya, Muhammad Adamu ya yi kira ga ƴan sanda a kasar su kare kansu idan an kai musu hari

- IGP Adamu ya yi wannan furucin ne cikin jawabin da ya yi a hedkwatar rundunar da ke Abuja bayan ziyarar ganin ido

- Shugaban ƴan sandan ya ce ɓata garin da suka shigar rigar zanga-zanga nufin su shine karya wa ƴan sanda kwarin gwiwa

Babban sifetan ƴan sandan Najeriya, IGP, Mohammed Adamu a ranar Juma'a ya faɗa wa jami'an rundunar su kare kansu idan aka kai musu hari a gari kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Shugaban ƴan sandan ya yi jawabi ne a hedkwatar rundunar da ke Abuja bayan ziyarar zagaye da ya yi don ƙarfafawa gwiwar jami'an da wasunsu sun dena fita tituna.

Adamu ya kuma ce masu zanga-zangar EndSARs sunyi yunkurin rage wa ƴan sandan ƙwarin gwiwa amma rundunar za ta fito da tsarin tallafawa wadanda suka rasa rayukansu.

Ku kare kanku idan an kawo muku hari, IGP ya fada wa 'Yan sanda
Babban Sifetan 'Yan sanda, Mohammed Adamu. Hoto: @PoliceNG
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: 'Farautar 'yan bindiga suke yi' - Gwamnatin Kaduna ta yi karin haske kan jiragen sojoji da ke shawagi a jihar

A baya-bayan nan ɓata gari da suka shiga rigar zanga-zangar EndSARs sun rika kaiwa ƴan sanda hari a sassan ƙasar.

Daily Trust ta ruwaito cewa ƴan sanda 22 ne fusatattun masu zanga-zangar suka kashe a sassan ƙasar.

KU KARANTA: Zulum ya bayyana matakin da zai dauka kan ɓata garin da aka yi haya don yin zanga zanga a Borno

An kuma ƙone ofishin ƴan sanda 205 tare da wasu kamfanoni da gine-ginen gwamnati da na ƴan kasuwa masu muhimmanci.

A wani labarin, 'yar majalisar mai wakiltar mazaɓar Amuwo Odofin ta 1 a Jihar Legas, Mojisola Alli-Macaulay ta ce mafi yawancin matasan Najeriya cikin mayen ƙwayoyi suke a kullum.

Alli-Macaulay ta bayyana hakan ne yayin zaman majalisar jihar Legas da aka yi kan sata da ɓarna da ɓata gari suka yi sakamakon zanga-zangar EndSARs a cewar rahoton The Punch.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel