EndSARS: Legos ta sake rikicewa yayin da yan tawaye suka lalata motocin BRT, suka fasa shaguna

EndSARS: Legos ta sake rikicewa yayin da yan tawaye suka lalata motocin BRT, suka fasa shaguna

- An lalata motocin BRT da dama a Lagos ranar Talata, 27 Oktoban shekarar 2020

- Yan tawayen sun aikata barnar tasu a Mil 2 wani bangare na jahar ta Legas

- Rahotanni sun bayyana cewa a fasa shaguna da kantina da dama a yankin

Ga dukkan alamu yan tawaye a Legas basu gama da lalata kayayyaki ba inda suka waiwayi yankin Mil 2 suka kuma ci gaba da barna a ranar Talata 27 ga Oktoba a yankin da ke jihar Legas.

A wani rahoto mai ban tsoro da PM News ta fitar ya nuna cewa wasu gungun 'yan daban sun lalata da yawa daga cikin motocin BRT kamar yadda Legit.ng ta ruwaito.

EndSARS: Lagos ta sake rikicewa yayin da yan tawaye suka lalata motocin BRT, suka fasa shaguna
EndSARS: Lagos ta sake rikicewa yayin da yan tawaye suka lalata motocin BRT, suka fasa shaguna. Hoto: theinfostride.com
Asali: UGC

DUBA WANNAN: Mutum 5 sun mutu yayin rabon kuɗin da suka tsinnta a ma'ajiyar kayan tallafin korona

An kuma hango su da adduna suna fashe shaguna a yankin inda rikicin ya barke har Owade axis kan hanyar Ikorudu.

Wannan ya tilasta Primero, mai kula da motocin BRT fara tunanin dakatar da da al'amura saboda gudun kada a ci gaba da lalata musu motoci.

Sai dai kuma, wani jami'in tsaro da ya nemi a sakaya sunansa ya shaidawa yan jarida cewa tuni aka girke jami'an yan sanda a yankin don saita al'amura da dawo da zaman lafiya.

KU KARANTA: Abin da yasa muka jinkirta rabon tallafin korona a Sokoto - Gwamna Tambuwal

A makamancin hakan, wasu fusatattun matasa sun sauke fushinsu akan gwamnan jihar, Babajide Sanwa-Olu.

Matasan kamar yadda jaridar This Day ta rawaito, sun cinna wa gidan mahaifiyar Sanwa-Olu wuta ranar Laraba 21 ga Oktoban 2020.

A wani labarin dabam, nn sace ma'aikacin jami'ar Gwamnatin Tarayya ta Dutse (FUD), jihar Jigawa mai suna Shehu Abdulhamid a jihar Kano kamar yadda LIB ta ruwaito.

Mai magana da yawun jami'ar, Abdullahi Bello ya tabbatar da afkuwar lamarin a ranar Juma'a 23 ga watan Oktoban shekarar 2020.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel