Gwamnan Osun ya bai wa masu satar kayan tallafi wa'adi, ya sanar da abinda za su iya fuskanta

Gwamnan Osun ya bai wa masu satar kayan tallafi wa'adi, ya sanar da abinda za su iya fuskanta

- Gwamnan jihar Osun, Adegboyega Oyetola ya umarci masu zanga-zangar EndSARS da su dawo da duk abinda suka sata yayin zanga-zangar

- A ranar Lahadi, 25 ga watan Oktoba ne gwamnan ya umarci bata-garin, inda ya basu kwanaki 3 su mayar da komai da suka dauka

- Ya ce lallai duk wanda bai mayar da abubuwan da ya dauka ba cikin kwanaki uku, zai fuskanci hukunci mai tsanani

Rahotanni sun nuna yadda bata-gari suka saci dukiyoyin gwamnati, ciki har da kayan abincin tallafin COVID-19 a ranar Asabar. An umarci bata-garin wadanda suka yi satar da sunan zanga-zangar EndSARS da su mayar da duk abubuwan da suka sata cikin kwana 3.

Gwamnan jihar Osun, Adegboyega Oyetola ne ya bayar da wannan umarnin a ranar Lahadi, 25 ga watan Oktoba, yayin da yake zagaye jihar don ganin barnar da suka yi a jiharsa.

Ya ce idan har basu dawo da duk abubuwan da suka sata ba cikin kwana 3, to tabbas zasu fuskanci fushin hukuma.

KU KARANTA: Tallafin Covid-19: An gane mahaifina ba shine matsalar Najeriya ba - Zahra Buhari

Gwamnan Osun ya bai wa masu satar kayan tallafi wa'adi, ya sanar da abinda za su iya fuskanta
Gwamnan Osun ya bai wa masu satar kayan tallafi wa'adi, ya sanar da abinda za su iya fuskanta. Hoto daga @TheCable
Asali: Facebook

Ya ce su mayar da kayan da suka sata zuwa fadar sarki mafi kusa da su, Legit.ng ta wallafa.

KU KARANTA: Yanzu-yanzu: 'Yan sanda sun halaka mutum 6 da ake zargin 'yan Boko Haram ne

A wani labari na daban, Rochas Okorocha, tsohon gwamnan jihar Imo, ya yi bayani dalla-dalla a kan dalilan da ke hassalar da matasa suna tada hankulan jama'a, asarar dukiya da kuma tayar da zaune tsaye da sunan zanga-zangar EndSARS.

A ranar Juma'a, 23 ga watan Oktoba, yayin da Sanatan, kuma tsohon gwamnan, wanda yanzu haka shine mai wakiltar mazabar Imo ta yamma, ya yi hira da manema labarai a Abuja, inda yace mulkin kama-karya, zalunci, kunci, bala'i da yunwa ne dalilin da ya tunzuro matasa suka mayar da zanga-zangar EndSARS tashin hankali.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel