Allah ya yiwa shahrarren mawaki, Hassan Wayam, rasuwa

Allah ya yiwa shahrarren mawaki, Hassan Wayam, rasuwa

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un! Allah ya yiwa shahrarren mawakin Hausa, Hassan Wayam rasuwa.

Wayan ya rasu ne yana mai shekaru 64 a daren Juma'a a asibiti bayan dogon jinyan da yayi fama da shi, cewar majiyoyi.

Hassan Wayam wanda aka haifa 1956 a kauyen Gwadda dake karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara, ya fara waka ne a garin Mayanci sannan ya koma Zariya a 1969, Daily Nigerian ta ruwaito.

Ya shahara a Arewacin Najeriya inda yake waka a taruka.

Wakokinsa mafi shahara sun hada da “Tana Kukan Kurciya”, “Ba Ni Ne Na Fada Ba, Hassan Wayam Ne Ya Fada”, “Kowac Ci Kurciya”, da sauransu.

Allah ya yiwa shahrarren mawaki, Hassan Wayam, rasuwa
Allah ya yiwa shahrarren mawaki, Hassan Wayam, rasuwa Credit: Whatsapp SH
Asali: UGC

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng