Da duminsa: 'Yan daba sun kai hari sakatariyar karamar hukumar Iwo a Osun

Da duminsa: 'Yan daba sun kai hari sakatariyar karamar hukumar Iwo a Osun

- Wasu matasa da ake kyautata zaton 'yan daba ne sun afka sakatariyar karamar hukumar Iwo a jihar Osun

- Matasan sun cinna wa motocci da dama wuta sun kuma shiga ofisoshi sun sace kayayyaki tare da lalata wasu

- Wani jami'in gwamnati a jihar a tabbatar da afkuwar lamarin amma ya bukaci a sakayya sunansa

'Yan daba a ranar Asabar sun kai hari sakatariyar karamar hukumar Iwo ta Kudu a jihar Osun da ke Kudu maso yammacin Najeriya.

Yayin harin, 'yan daban sun lalata kayayyaki sannan sun cinnawa motocci wuta, kamar yadda majiya daga fadar Oluwo na Iwo suka tabbatar.

Da duminsa: 'Yan daba sun kai hari sakatariyar karamar hukumar Iwo a Osun
Da duminsa: 'Yan daba sun kai hari sakatariyar karamar hukumar Iwo a Osun. Hoto daga @MobilePunch
Asali: UGC

DUBA WANNAN: Rayuka 69 suka salwanta sakamakon zanga zanga EndSARS, inji Buhari

Wasu da abin ya faru a idonsu sun shaidawa The Punch cewa 'yan daban sun kuma sace kayayyaki daga ofisoshin da ke sakatariyar.

Daya daga cikin mambobin majalisar da ya nemi a sakayya sunansa shima ya tabbatar da harin.

'Yan daban da suka fito da yawa sun kuma kutsa cikin wani gidan gona mai suna Tuns Farm da ke kan titin Osogbo/Ikirun sun sace kayayyaki.

KU KARANTA: Mazauna Kwara suma sun kwashi kayan tallafin korona daga wurin ajiya (Bidiyo)

Wani hadimin shugaban karamar hukumar Iwo ta Kudu, wanda shima ya nemi a sakayya sunansa ya tabbatar cewa wasu 'yan daba sun kai hari a sakatariyar karamar hukumar ta Iwo.

A wani labarin, Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu ya sassauta dokar hana fita na awa 24 da aka saka a jihar a lokacin da rikici ya yi kamari a jihar sakamakon zanga zangar EndSARS.

Sanwo-Olu ya bayyana hakan ne yayin wata jawabi da ya yi a ranar Juma'a.

Da ya ke jawabi bayan ya ziyarci wuraren da aka yi rikici a jihar, gwamnan ya ce daga ranar Asabar mutane suna iya fita daga karfe 8 na safe zuwa karfe shida na yamma.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel