Hotuna: Harkokin kasuwanci sun koma daidai bayan cire dokar kulle a Jos

Hotuna: Harkokin kasuwanci sun koma daidai bayan cire dokar kulle a Jos

- Kamar yadda rikicin EndSARS ya barke a jihar Filato, kowa yana ta tunanin kafin al'amura su dawo kamar da za su iya daukar lokaci mai tsawo

- Amma abin ba haka bane, matasa sun yi ba-zata, inda suka kwantar da hankulansu kuma titunan sun koma fes tamkar babu abinda ya taba faruwa

- Yanzu haka, titin Ahmadu Bello kusa da titin Bauchi ya koma kamar da, hatta bankuna da wuraren shige da ficen kudade sun cigaba da harkokinsu

Rayuwa ta fara komawa daidai a kananan hukumomin Jos ta Arewa da kuma Jos ta kudu awanni kadan bayan sakakullen awanni 24 a kananan hukumomin guda biyu da ke jihar Filato.

A ranar Talata ne gwamna Simon Lalong yasa kullen awanni 24 bayan rikicewar garin sakamakon zanga-zangar EndSARS da ta koma tashin hankali a kan titin Ahmadu Bello.

Hotuna: Harkokin kasuwanci sun koma daidai bayan cire dokar kulle a Jos
Hotuna: Harkokin kasuwanci sun koma daidai bayan cire dokar kulle a Jos. Hoto daga @Dailytrust
Asali: Twitter

Kowa ya koma bakin sana'arsa a kasuwar Terminus da ke kan titin Ahmadu Bello, layin Bauchi, kuma tashar motar Bukuru ta koma kamar da.

Hotuna: Harkokin kasuwanci sun koma daidai bayan cire dokar kulle a Jos
Hotuna: Harkokin kasuwanci sun koma daidai bayan cire dokar kulle a Jos. Hoto daga @Dailytrust
Asali: Twitter

KU KARANTA: 'Yan bindiga sun kai hari, sun sace matashi mai shekaru 24 a Abuja

Haka kuma bankuna da sauran wuraren shige da ficen kudi sun cigaba da aiwatar da ayyuka tamkar babu abinda ya faru, Daily Trust ta tabbatar.

Hotuna: Harkokin kasuwanci sun koma daidai bayan cire dokar kulle a Jos
Hotuna: Harkokin kasuwanci sun koma daidai bayan cire dokar kulle a Jos. Hoto daga @Dailytrust
Asali: Twitter

KU KARANTA: EndSARS: Hukumar DSS ta magantu a kan zargin da ake mata, ta yi karin haske

A wani labari na daban, hedkwatar tsaro tace Operation Lafiya Dole ta samu nasarar ragargazar 'yan Boko Haram 4, kuma ta kwace bindigogi AK47 a hannunsu, yayin da suka je aiki kauyen Sawa dake karamar hukumar Nganzai dake jihar Borno.

Kakakin rundunar sojin, John Enenche, ya sanar da hakan yayin da yake bayar da bayani a kan ayyukan da rundunar suka yi a ranar Alhamis a Abuja.

A cewarsa, rundunar Operation Lafiya Dole ta sama da kasa sun yi nasarar fatattakar 'yan ta'adda da dama da ke maboyarsu cikin sati daya a Arewa maso gabas.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng