Bata gari sun kona ofisoshin yan sanda 10 - Kakakin hukumar yan sanda

Bata gari sun kona ofisoshin yan sanda 10 - Kakakin hukumar yan sanda

- Kakakin hukumar yan sandan jihar Legas ya bayyana adadin ofishohinsu da matasa suka kona

- An yi asarar rayuka da dama tun lokacin da Sojoji suka budewa masu zanga-zanga wuta

- Hakan ya fusata matasa kuma ya ingiza su kai hare-hare ofishohin gwamnati

Hukumar yan sandan jihar Legas ta bayyana cewa akalla ofishohin yan sanda 10 aka bankawa wuta tun lokacin da bata gari suka kwace zanga-zangar #EndSARS a jihar.

Kakakin hukumar yan sandan jihar, Muyiwa Adejobi, a jawabin da ya saki jiya ya bayyana yadda matasa suka kai hare-hare jihar.

Ya ce akalla ofishohin yan sanda 10 aka bankawa wuta tun lokacin da aka fara wannan rikici.

Yace: "Bata gari, wadanda suke cigaba da tayar da tarzoma a jihar Legas da sunan zanga-zangar #EndSARS, sun kashe yan sanda biyu a ofishin yan sandan Orile, sun jikkata da dama kuma sun kona ofishohin yan sanda 10 a jihar."

"Daga cikin ofishohin yan sandan da aka kai hari akwai na unguwannin Idimu, Igando, Layeni, Denton, Ilenbe Hausa, Ajah, Amukoko, Ilasa, Cele Outpost under Ijesha, ofishin SARS dake Ajegunle, Ebute-Ero Mushin (Olosan), Ojo da Ajegunle."

KU DUBA: Sarkin Musulmi ya umurci Musulmai su yiwa Najeriya addu'a na musamman ranar Juma'a

Bata gari sun kona ofisoshin yan sanda 10 - Kakakin hukumar yan sanda
Bata gari sun kona ofisoshin yan sanda 10 - Kakakin hukumar yan sanda Credit: @ThisDay
Asali: Twitter

KU KARANTA: Rikicin #EndSARS: Jerin wurare 23 da bata gari suka kai hari ko bankawa wuta

A bangare guda, wasu bata gari sun bankawa hedkwatar gidan jaridar The Nation, mallakin babban jigon APC, Asiwaju Bola Tinubu, wuta.

Yanzu haka ginin kamfanin dake Matori a jihar Legas na ci da wuta, a cewar rahoton The Cable Hakan ya biyo bayan kona gidan talabijin na TVC, duka mallakin dan siyasan.

Ana kyautata zaton cewa ana kai wadannan hare-haren dukiyoyin Bola Tinubu don manufa ta siyasa.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng