EndSARS: Na tattauna da Buhari - Shugaban Ghana, Akufo-Addo

EndSARS: Na tattauna da Buhari - Shugaban Ghana, Akufo-Addo

- Shugaba Nana Akufo-Addo na kasar Ghana ya bayyana cewa Shugaba Buhari a shirye ya ke ya yi sulhu da masu zanga-zanga

- Akufo-Addo ya sanar da hakan ne cikin wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na dandanlin sada zumunta ta Twitter

- Shugaba Akufo-Addo ya yi kira ga masu zanga-zanga da 'yan sanda su guji tashin hankali kana ya mika sakon ta'aziyyarsa da wadanda suka rasu

Shugaban Kasar Ghana, Nana Akufo-Addo, ya yi kira ga Shugaba Buhari da yin sulhu da masu zanga-zangar #ENDSARS.

Ya yi gargadin cewa rikici bashi zai kawo karshen matsalar zanga zangar da ake don nuna bacin rai kan muguntar yan sanda.

Akufo-Addo ya ce ya yi magana da Shugaba Buhari kan matsalar kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Twitter a ranar Laraba 21 ga watan Oktoba.

DUBA WANNAN: Da duminsa: 'Yan sanda sun kama wanda ake zargi da sata a banki a Legas

Shugaban na Ghana ya cewa shugaba Buhari a shirye yake don yin sulhu.

Na yi magana da Buhari, ya ce zai tattauna - Shugaban Ghana, Nana-Akufo
Shugaba Muhammadu Buhari da Shugaba Nana-Akufo. Hoto daga @channelstv
Asali: Twitter

Ya wallafa a shafinsa na Twitter, "Nabi sahun mutane masu kima wajen kira da a zauna lafiya, da kuma amfani da sulhu wajen kawo karshen rikicin #ENDSARS a Najeriya. Nayi magana da shugaba Buhari kuma ya tabbatar min a shirye yake don yin sulhu, kuma tuni shiri yayi nisa don kawo karshen matsalar".

"Tashin hankali, daga bangaren masu zanga-zanga ko 'yan sanda ba zai warware matsalar ba. Ina mika sakon ta'aziyya ga iyalan wadanda suka rasa ;yan uwansu sannan ina yi wa wadanda suka samu rauni fatan samun sauki cikin gaggawa."

KU KARANTA: 'Yan daba sun mamaye fadar Sarkin Legas, sun kwace sandar ikonsa

A wani labarin, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya shawarci shugaba Muhammadu Buhari da ya yi wa masu zanga-zanga jawabi. Ya gargadi cewa kada shugaban yayi amfani da karfin hukuma akan masu zanga-zangar #ENDSARS.

Dan takarar jam'iyyar PDP a zaben shugaban kasa daya gabata ya wallafa hakan ne a shafinsa na Twitter ranar Talata.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164