Yanzu-yanzu: Bata gari sun sake bankawa gidan jarida mallakin Tinubu, The Nation, wuta

Yanzu-yanzu: Bata gari sun sake bankawa gidan jarida mallakin Tinubu, The Nation, wuta

- Fusatattun matasa da bata gari sun cigaba da kai hare-hare kamfanoni a jihar Legas

- Bayan bankawa gidan talabijin TVC wuta, sun garzaya gidan jaridar The Nation

- Harbin matasa masu zanga-zanga da Sojoji suka yi ya tayar da wannan tarzoman

Wasu bata gari sun bankawa hedkwatar gidan jaridar The Nation, mallakin babban jigon APC, Asiwaju Bola Tinubu, wuta.

Yanzu haka ginin kamfanin dake Matori a jihar Legas na ci da wuta, a cewar rahoton The Cable

Hakan ya biyo bayan kona gidan talabijin na TVC, duka mallakin dan siyasan.

Ana kyautata zaton cewa ana kai wadannan hare-haren dukiyoyin Bola Tinubu don manufa ta siyasa.

Yanzu-yanzu: Bata gari sun sake bankawa gidan jarida mallakin Tinubu, The Nation, wuta
Yanzu-yanzu: Bata gari sun sake bankawa gidan jarida mallakin Tinubu, The Nation, wuta www.sandiegouniontribune.com
Asali: UGC

DUBA NAN: Kwana hudu bayan harbinsa, babban dan siyasa a Kogi, Adejo, ya mutu

Mun kawo muku rahoton cewa matasan jihar Legas sun afka gidan talabijin TVC News wanda ake zargin mallakin tsohon gwamnan Legas, Asiwaju Bola Tinubu, ne.

Bidiyon da daya daga cikin ma'aikatan kamfanin jaridar ta saki, Precious Amayo, ya nuna yadda wadanda ke cikin shiri suka gudu daga studiyo ana tsakiyan shirin YourView.

Hakazalika bidiyon Arise TV ya nuna yadda gidan jaridan ke ci bal-bal

KU KARANTA: Kisan Lekki: Sarkin Musulmi ya umurci Musulmai su yiwa Najeriya addu'a na musamman ranar Juma'a

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel