Yanzu-yanzu: Buhari ya nada Sanusi Garba sabon shugaban hukumar kula da wutan lantarki a Najeriya

Yanzu-yanzu: Buhari ya nada Sanusi Garba sabon shugaban hukumar kula da wutan lantarki a Najeriya

- Majalisar dattawa ta yi zaman majalisa ranar Talata duk da rikicin zanga-zangan dake faruwa a kasar

- Majalisar ta karbi sakon shugaba Buhari kan sabon shugaban hukumar NERC da ya zaba

- Daga cikin wadanda ya zaba akwai maza biyu da mace daya

Shugaba Muhammadu Buhari ya zabi wadanda yake son a nada sabbin shugabannin hukumar lura da wutar lantarki a Najeriya watau NERC.

Shugaban kasar ya aike da sunayensu majalisar dokokin tarayya domin tabbatar da su.

Shugaban majalisar dattawa, Ahmed Ibrahim Lawan, ya karanta wasikar da Buhari ya aiko musu a zauren majalisa ranar Talata, 20 ga watan Oktoba, 2020.

Wadanda Buhari ya zaba sune:

1 . Engr. Sanusi Garba - Shugaba

2. Musiliu Olalekan Oseni - Mataimakin shugaba

3. Aisha Mahmud - Kwamishana

Bayan haka, Buhari ya aike da da sunan Chief Onyenuchi Nnamani, wakilin yankin kudu maso yamma, matsayin daya daga cikin mambobin hukumar kula da lamuran yan sanda watau Police Service Commision PSC.

Yanzu-yanzu: Buhari ya nada Sanusi Garba sabon shugaban hukumar kula da wutan lantarki a Najeriya
Yanzu-yanzu: Buhari ya nada Sanusi Garba sabon shugaban hukumar kula da wutan lantarki a Najeriya Hoto: @mobilepunch
Asali: Twitter

KU KARANTA: Gwamnatin Buhari za ta nemi bashin $11bn don gina layin dogon Legas-Calabar

DUBA NAN: An hanawa wani Likita Musulmi hakkin zama dan kasa saboda ya ki musafaha da mace

A bangare guda, majalisar dattawa, a ranar Talata ta yi kira ga Shugaba Muhammadu Buhari ya yi wa 'yan Najeriya jawabi nan take a kan zanga-zangar da matasa ke yi a jihohin kasar game da cin zali da 'yan sanda ke yi da kuma neman kawo gyara a gwamnati.

Majalisar ta kuma bukaci jami'an 'yan sanda su bawa matasa da ke zanga-zangar ta EndSARS kariya daga 'yan daba da ke neman mamaye zanga-zangar kamar yadda The Punch ta ruwaito.

Majalisar ta cimma wannan matsayar ne bayan wani takarda da Sanata Biodun Olujimi ya gabatar mai taken "EndSARS: Bukatar yin garambawul mai sahihanci."

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng