Yanzu-yanzu: An saka dokar hana fita -ba dare, ba rana- a jihar Legas

Yanzu-yanzu: An saka dokar hana fita -ba dare, ba rana- a jihar Legas

- Bayan kwanaki 12, gwamnatin Legas ta bi sahun Edo wajen sanya dokar ta baci

- An kona ofishin yan sanda dake Orile da safiyar Talata a Legas

- Gwamnan ya baiwa ma'aikata sa'o'i uku su koma gidajensu zuwa karfe 4 na rana

Labarin da ke shigo mana da duminsa na nuna cewa sakamakon zanga-zanga, kashe-kashe da kone-konen dake faruwa a jihar Legas, gwamnatin jihar ta saka dokar ta baci a dukkan sassan jihar.

Gwamnan jihar, Babajide Sanwo-Olu ya bayyana hakan a shafinsa na Tuwita, ranar Talata.

Ya baiwa mutanen jihar daman komawa gidajen daga yanzu zuwa karfe 4 saboda daga lokacin ba''a son ganin kowa a waje.

"Na zuba ido kan yadda zanga-zangan #EndSARS da aka fara cikin lumana ya zama wani abu daban da ka iya cutar da al'ummarmu, " yace

"An rasa rayuka da sassan jiki yayinda wasu bata gari ke cakuda da masu zanga-zanga domin aika-aika a jihar mu."

"A matsayinmu na gwamnati da ta san aikinta kuma ta shirya amsa bukatun #EndSARS, ba zamu zuba ido muna gani ana tayar da tarzoma a jiharmu ba."

"Saboda haka na sanya dokar hana fita na 24hrs a dukkan sassan jihar daga karfe 4 na yau, 20 ga Oktoba, 2020. Ba'a amince a ga kowa ba illa ma'aikata masu muhimmanci."

KU KARANTA: An hanawa wani Likita Musulmi hakkin zama dan kasa saboda ya ki musafaha da mace

Yanzu-yanzu: An saka dokan ta baci -ba dare, ba rana- a jihar Legas
Yanzu-yanzu: An saka dokan ta baci -ba dare, ba rana- a jihar Legas Hoto: @jidesanwoolu
Asali: Twitter

DUBA: Ya isa haka, ku sassauta - Tinubu ya yi kira ga masu zanga-zanga

Mun kawo muku cewa, wasu da ake zargin 'yan daba ne sun kona ofishin 'yan sanda da ke Apapa Iganmu a jihar Legas kamar yadda The Punch ta ruwaito.

Lamarin ya faru ne misalin karfe 9.45 na safiya a cewar wani da abin ya faru a idonsa. Mai magana da yawun karamar hukumar Orile-Iganmu, Ayo Micheal ya ce, "Eh, an kai hari ofishin 'yan sandan.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel