Yanzu-yanzu: An saka dokar hana fita -ba dare, ba rana- a jihar Legas

Yanzu-yanzu: An saka dokar hana fita -ba dare, ba rana- a jihar Legas

- Bayan kwanaki 12, gwamnatin Legas ta bi sahun Edo wajen sanya dokar ta baci

- An kona ofishin yan sanda dake Orile da safiyar Talata a Legas

- Gwamnan ya baiwa ma'aikata sa'o'i uku su koma gidajensu zuwa karfe 4 na rana

Labarin da ke shigo mana da duminsa na nuna cewa sakamakon zanga-zanga, kashe-kashe da kone-konen dake faruwa a jihar Legas, gwamnatin jihar ta saka dokar ta baci a dukkan sassan jihar.

Gwamnan jihar, Babajide Sanwo-Olu ya bayyana hakan a shafinsa na Tuwita, ranar Talata.

Ya baiwa mutanen jihar daman komawa gidajen daga yanzu zuwa karfe 4 saboda daga lokacin ba''a son ganin kowa a waje.

"Na zuba ido kan yadda zanga-zangan #EndSARS da aka fara cikin lumana ya zama wani abu daban da ka iya cutar da al'ummarmu, " yace

"An rasa rayuka da sassan jiki yayinda wasu bata gari ke cakuda da masu zanga-zanga domin aika-aika a jihar mu."

"A matsayinmu na gwamnati da ta san aikinta kuma ta shirya amsa bukatun #EndSARS, ba zamu zuba ido muna gani ana tayar da tarzoma a jiharmu ba."

"Saboda haka na sanya dokar hana fita na 24hrs a dukkan sassan jihar daga karfe 4 na yau, 20 ga Oktoba, 2020. Ba'a amince a ga kowa ba illa ma'aikata masu muhimmanci."

KU KARANTA: An hanawa wani Likita Musulmi hakkin zama dan kasa saboda ya ki musafaha da mace

Yanzu-yanzu: An saka dokan ta baci -ba dare, ba rana- a jihar Legas
Yanzu-yanzu: An saka dokan ta baci -ba dare, ba rana- a jihar Legas Hoto: @jidesanwoolu
Asali: Twitter

DUBA: Ya isa haka, ku sassauta - Tinubu ya yi kira ga masu zanga-zanga

Mun kawo muku cewa, wasu da ake zargin 'yan daba ne sun kona ofishin 'yan sanda da ke Apapa Iganmu a jihar Legas kamar yadda The Punch ta ruwaito.

Lamarin ya faru ne misalin karfe 9.45 na safiya a cewar wani da abin ya faru a idonsa. Mai magana da yawun karamar hukumar Orile-Iganmu, Ayo Micheal ya ce, "Eh, an kai hari ofishin 'yan sandan.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng