Sojoji sun suburbudi yan sanda masu amsan na goro hannun mutane a kan titi (Bidiyo)

Sojoji sun suburbudi yan sanda masu amsan na goro hannun mutane a kan titi (Bidiyo)

- - Yayinda gwamnati ke alkawarin gyare-gyare a hukumar yan sanda, wani bidiyo ya bayyana

- An ga bidiyon Sojoji na dukan yan sanda suna umurtansu su mayarwa mutane kudaden da suka karba daga hannunsu

Abubuwan mamaki na faruwa a Najeriya kulli yaumin musamman tsakanin jami'an tsaron Najeriya.

Wani faifan bidiyo ya bayyana a kafafen ra'ayi da sada zumunta inda aka yi takaddama tsakanin wasu jami'an sojoji da yan sanda a kan titi.

A cikin bidiyon, ana iya ganin lokacin da wani jami'in Soja yake marin dan sanda kan abinda yake yiwa fasinjojin dake wucewa.

Mun ji Sojan yana magana yana dukan dan sandan: "Me yasa kuke amsan kudi a hannunsu, ku mayar musu da kudadensu."

DUBA NAN: Shugaban 'yan sandan Najeriya ya gargadi jami’an rundunar a kan amfani da karfi kan masu zanga-zanga

Kalli bidiyon:

A wani labarin daban, wani fai-fain bidiyon jami'in dan sandan Najeriya ya bayyana a kafafen ra'ayi da sada zumunta inda aka gansa yana nadin tabar wiwi a bainar jama'a rike da bindigarsa.

Sojoji sun suburbudi yan sanda masu amsan na goro hannun mutane a kan titi (Bidiyo)
Sojoji sun suburbudi yan sanda masu amsan na goro hannun mutane a kan titi (Bidiyo) Credit: @bakintiti
Asali: Twitter

DUBA NAN: Gwamnan Yobe ya yiwa mutumin da ya mayar da kudi N1.7m kyauta mai tsoka

Wannan bidiyon ya bayyana ne lokacin da matasan Najeriya ke zanga-zangan neman sauyi a hukumar yan sandan Najeriya saboda irin cin zarafin da suke yiwa yan Najeriya.

Masu sharhi kan lamuran yau da kullum sun bayyana cewa ire-iren wadannan yan sanda ke kashe matasa bayan sun bugu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng