Da duminsa: FG ta sanar da ranar bude sansanonin horas da 'yan NYSC

Da duminsa: FG ta sanar da ranar bude sansanonin horas da 'yan NYSC

- Gwamnatin tarayya ta bada umurnin a bude sansanonin bawa masu yi wa kasa hidima horo a ranar 10 ga watan Nuwamba

- Sanarwar ta fito ne daga bakin Ministan Matasa da Cigaban Wasanni, Sunday Dare cikin wani sako da ya wallafa a Twitter a ranar Alhamis

- Ministan Matasan ya ce gwamnati za ta tanadi matakan dakile yaduwar cutar korona a sansanonin bawa masu yi wa kasa hidimar horo

Da duminsa: FG ta sanar da ranar bude sansanonin horas da 'yan NYSC
'Yan NYSC a Najeriya. Hoto daga @PremiumTimesng
Asali: Twitter

KU KARANTA: Gwamnan jihar Gombe ya nada dan kabilar Igbo a matsayin hadiminsa (Hotuna)

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta amince da bude dukkan sansanonin horas da masu yi wa kasa hidima ta NYSC a ranar 10 ga watan Nuwamban 2020.

Ministan Matasa da Cigaban Wasanni, Sunday Dare ne ya sanar da hakan a shafinsa na Twitter a ranar Alhamis.

Ya rubuta, "An amince da bude sansanonin horas da wadanda za su yi wa kasa hidima a ranar 10 ga watan Nuwamban 2020. Za a samar da matakin dakile yaduwar Covid 19."

DUBA WANNAN: An bayyana ranar buɗe makarantun gaba da sakandare a jihar Kano

A ranar 18 ga watan Maris ne gwamnatin tarayyar Najeriya ta bada umurnin rufe dukkan sansanonin horas da masu yi wa kasa hidiman don fargabar yaduwar annobar korona.

A wani labarin daban, Gwamna Babagana Zulum na jihar Borno a ranar Talata ya amince a ɗauki sabbin malamai 776 don inganta ilimi a makarantun gwamnatin jihar.

Gwamnan ya sanar da hakan ne jim kadan bayan gana wa da ya yi da jami'an Ma'aikatar Ilimi na jihar a gidan gwamanti da ke Maiduguri.

Gwamnan da yace malamai su koma aiki ranar 1 ga watan Nuwamba ya kara da cewa za a bada umurnin ɗaukan sabbin malamai nan take bayan kammala aikin tantance su da ake a jihar.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164