Hotuna: Ango ya garzaya wurin zanga-zangar EndSars daga wurin ɗaurin aurensa

Hotuna: Ango ya garzaya wurin zanga-zangar EndSars daga wurin ɗaurin aurensa

- Wani ango a Najeriya ya tafi wurin zanga-zangar EndSars a ranar da aka ɗaura masa aure ko kaya bai canja ba

- Angon ya wallafa hotunan sa sanye da kayan da aka ɗaura masa aure ɗauke da takarda da cewa 'ku rushe rundunar SARs yanzu'

- Matasa da dama a jihohi daban-daban a Najeriya sun kwashe kwanaki suna zanga-zangar neman ganin an rushe SARs tare da yin wasu sauye-sauye a rundunar ƴan sanda

Hotuna: Ango ya garzaya wurin zanga-zangar EndSars daga wurin ɗaurin aurensa. Hoto: @OgebeniKunle1
Hotuna: Ango ya garzaya wurin zanga-zangar EndSars daga wurin ɗaurin aurensa
Asali: Twitter

Hotuna: Ango ya garzaya wurin zanga-zangar EndSars daga wurin ɗaurin aurensa
Hotuna: Ango ya garzaya wurin zanga-zangar EndSars daga wurin ɗaurin aurensa. Hoto: @OgebeniKunle1
Asali: Twitter

Wani ɗan Najeriya ya shiga ya zanga-zangar da matasa suka yi a kasar na neman rushe rundunar ƴan sanda ta musamman na SARs a ranar da aka ɗaura masa aure a Legas.

An ɗauki hotunan mutumin mai suna @OgebeniKunle1 a Twitter sanye da kayan da ya tafi wurin ɗaurin aure da su a jikinsa yana rike da takarda ta zanga-zanga.

DUBA WANNAN: Dattijo mai shekaru 106 ya auri sahibarsa mai shekaru 35 (Hotuna)

Hotuna: Ango ya garzaya wurin zanga-zangar EndSars daga wurin ɗaurin aurensa
Hotuna: Ango ya garzaya wurin zanga-zangar EndSars daga wurin ɗaurin aurensa. Hoto: @OgebeniKunle1
Asali: Twitter

Hotuna: Ango ya garzaya wurin zanga-zangar EndSars daga wurin ɗaurin aurensa
Hotuna: Ango ya garzaya wurin zanga-zangar EndSars daga wurin ɗaurin aurensa. Hoto: @OgebeniKunle1
Asali: Twitter

KU KARANTA: Da ɗuminsa: Akeredolu ya gana da Buhari, ya bukaci mataimakinsa ya yi murabus

Hakan na nuna akwai alamun bayan ɗaurin auren bai wuce ko ina ba sai wurin zanga-zangar domin shima ya bada tasa irin gudummawar.

A hotunan da ya wallafa a shafinsa na Twitter, ya rubuta cewa: "A yau na shiga zanga-zangar #EndSARS bayan an ɗaura min aure a kotu. Kada SARS su kashe wa matata mijin ta."

A wani labarin daban, mutum tara ne suka riga mu gidan gaskiya yayin da wasu uku suka jikkata sakamakon mummunan hatsarin mota da ya faru a Kano kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Zubairu Mato, Kwamandan Hukumar Kiyayye Hadurra ta Kasa, FRSC, a jihar cikin wata sanarwa da ya ce hatsarin ya faru ne misalin karfe 9 na safe da ya ritsa da mota da adaidaita sahu a hanyar Kano zuwa Zaria a kauyen Imawa da ke karamar hukumar Kura.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164