Zaben Ondo: Abubuwa 11 da ya dace ka sani game dan takarar jam'iyyar, APC Rotimi Akeredolu

Zaben Ondo: Abubuwa 11 da ya dace ka sani game dan takarar jam'iyyar, APC Rotimi Akeredolu

- Gwamna Rotimi Akeredolu na daya daga cikin manyan 'yan takarar a zaben gwamnan jihar Ondo, ya lashe tikitin takarar APC a ranar Litinin 20 ga watan Yulin 2020

- Gwamnan mai ci a yanzu ya lashe zaben fidda gwani ja jam'iyyar bayan lashe kuri'u mafi yawa a dukkan kananan hukumomi 18 na jihar inda ya doke babban abokin karawarsa, Cif Oke da wasu 'yan takarar.

- A yayin da gwamnan ke neman yin tazarce, wasu 'yan takara ciki har da mataimakinsa, Agoola Ajayi na cikin masu son karbe kujerarsa

Zaben Ondo: Abubuwa 11 da ya dace ka sani game dan takarar jam'iyyar, APC Rotimi Akeredolu
Dan takarar gwamnan APC a jihar Ondo Rotimi Akeredolu: Hoto: @RotimiAkeredolu
Asali: Twitter

Legit.ng ta kawo muku wasu muhimman abubuwa 11 game da dan takarar jam'iyyar APC a zaben gwamnan jihar Ondo na shekarar 2020.

1. Akeredolu ya fito ne daga karamar hukumar Owo a mazabar Ondo North.

2. An haife shi a ranar 21 ga watan Yulin 1956 a garin Owo, sunan mahaifinsa Reverend J. Ola Akeredolu mahaifiyarsa kuma Grace B. Akeredolu.

DUBA WANNAN: Dattijo mai shekaru 106 ya auri sahibarsa mai shekaru 35 (Hotuna)

3. Ya yi karatun frimari a makarantar gwamnati a garin Owo. Ya makarantun sakandare guda 3 wato Aquinas College, Akure, Loyola College, Ibadan da Comprehensive High School, Ayetoro.

4. Ya kuma yi digiri a fanin lauya a Jami'ar Ife (yanzu Jami'ar Obafemi Awolowo).

5. Ya samu lasisin fara aikin lauya a 1978 kuma ya zama SAN a 1988.

6. An nada shi attoney janar na jihar Ondo daga 1997 zuwa 1999.

7. A shekarar 2008, ya yi aiki a matsayin shugaban kungiyar lauyoyi ta Najeriya (NBA).

KU KARANTA: Kiran dan majalisa dan luwadi, jahili a Facebook: Kotu ta tsare matashi a Gombe

8. Akeredolu na cikin masu kula da kamfanin aikin lauya na Olujinmi & Akeredolu da suka kafa tare da Cif Akin Olujinmi tsohon attoney janar kuma ministan shari'a na Najeriya.

9. Akeredolu ya yi takarar gwamna a karkashin jam'iyyar Action Congress of Nigeria (ACN) a zaben 2013.

10. An zabe shi gwamna a karo na farko a shekarar 2016 bayan ya kada dan takarar jam'iyyar PDP, Etitayo Jegede.

11. Yana auren Betty Anywanwu-Akeredolu 'yar asalin jihar Imo. Sun hadu wurin yi wa kasa hidima NYSC kuma suna da yara hudu.

A wani labrin daban, Ƙungiyar Shugabannin Ƙananan Hukumomi ta Najeriya, ALGON, ta tsige mataimakin ta na ƙasa Mohammed Aliyu Soba daga muƙaminsa.

Mr Soba shine shugaban ƙaramar hukumar Soba a jihar Kaduna kuma shugaban kungiyar reshen jihar.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164