Zaben Ondo: Abubuwa 11 da ya dace ka sani game dan takarar jam'iyyar, APC Rotimi Akeredolu

Zaben Ondo: Abubuwa 11 da ya dace ka sani game dan takarar jam'iyyar, APC Rotimi Akeredolu

- Gwamna Rotimi Akeredolu na daya daga cikin manyan 'yan takarar a zaben gwamnan jihar Ondo, ya lashe tikitin takarar APC a ranar Litinin 20 ga watan Yulin 2020

- Gwamnan mai ci a yanzu ya lashe zaben fidda gwani ja jam'iyyar bayan lashe kuri'u mafi yawa a dukkan kananan hukumomi 18 na jihar inda ya doke babban abokin karawarsa, Cif Oke da wasu 'yan takarar.

- A yayin da gwamnan ke neman yin tazarce, wasu 'yan takara ciki har da mataimakinsa, Agoola Ajayi na cikin masu son karbe kujerarsa

Zaben Ondo: Abubuwa 11 da ya dace ka sani game dan takarar jam'iyyar, APC Rotimi Akeredolu
Dan takarar gwamnan APC a jihar Ondo Rotimi Akeredolu: Hoto: @RotimiAkeredolu
Asali: Twitter

Legit.ng ta kawo muku wasu muhimman abubuwa 11 game da dan takarar jam'iyyar APC a zaben gwamnan jihar Ondo na shekarar 2020.

1. Akeredolu ya fito ne daga karamar hukumar Owo a mazabar Ondo North.

2. An haife shi a ranar 21 ga watan Yulin 1956 a garin Owo, sunan mahaifinsa Reverend J. Ola Akeredolu mahaifiyarsa kuma Grace B. Akeredolu.

DUBA WANNAN: Dattijo mai shekaru 106 ya auri sahibarsa mai shekaru 35 (Hotuna)

3. Ya yi karatun frimari a makarantar gwamnati a garin Owo. Ya makarantun sakandare guda 3 wato Aquinas College, Akure, Loyola College, Ibadan da Comprehensive High School, Ayetoro.

4. Ya kuma yi digiri a fanin lauya a Jami'ar Ife (yanzu Jami'ar Obafemi Awolowo).

5. Ya samu lasisin fara aikin lauya a 1978 kuma ya zama SAN a 1988.

6. An nada shi attoney janar na jihar Ondo daga 1997 zuwa 1999.

7. A shekarar 2008, ya yi aiki a matsayin shugaban kungiyar lauyoyi ta Najeriya (NBA).

KU KARANTA: Kiran dan majalisa dan luwadi, jahili a Facebook: Kotu ta tsare matashi a Gombe

8. Akeredolu na cikin masu kula da kamfanin aikin lauya na Olujinmi & Akeredolu da suka kafa tare da Cif Akin Olujinmi tsohon attoney janar kuma ministan shari'a na Najeriya.

9. Akeredolu ya yi takarar gwamna a karkashin jam'iyyar Action Congress of Nigeria (ACN) a zaben 2013.

10. An zabe shi gwamna a karo na farko a shekarar 2016 bayan ya kada dan takarar jam'iyyar PDP, Etitayo Jegede.

11. Yana auren Betty Anywanwu-Akeredolu 'yar asalin jihar Imo. Sun hadu wurin yi wa kasa hidima NYSC kuma suna da yara hudu.

A wani labrin daban, Ƙungiyar Shugabannin Ƙananan Hukumomi ta Najeriya, ALGON, ta tsige mataimakin ta na ƙasa Mohammed Aliyu Soba daga muƙaminsa.

Mr Soba shine shugaban ƙaramar hukumar Soba a jihar Kaduna kuma shugaban kungiyar reshen jihar.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel