Shugaba Buhari ya ware N10b domin a kidaya yawan mutanen Najeriya

Shugaba Buhari ya ware N10b domin a kidaya yawan mutanen Najeriya

- Gwamnatin Buhari ta ware kudi da nufin a fara aikin kidayar ‘Yan Najeriya

- NPC za ta soma aikin EAD domin sharar fagen gano yawan mutanen kasa

- Shugaban Hukumar NPC, Oyetunji ya ce za a soma wannan aiki kafin zabe

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince a fitar wa hukumar kidaya ta kasa watau NPC, kudi domin aikin EAD a wasu bangarorin Najeriya.

The Nation ta ce Mai girma Muhammadu Buhari ya bada umarnin a warewa hukumar NPC Naira biliyan 10 domin kidaya a kananan hukumomi 546.

Ana yin wannan aiki na EAD ne domin a tsara yadda za a ji dadin kidaya mutanen da ke Najeriya.

KU KARANTA: Buhari ya yi magana game da salon nadin kujeru

Haka zalika shugaban kasar ya bada umarni a ware Naira biliyan 4.5 a kasafin kudin shekara mai zuwa domin ayi aikin kidayar mutanen da ke kasar nan.

Mukaddashin shugaban NPC na kasa, Dr. Eyitayo Oyetunji, ya shaidawa ‘yan jarida wannan lamari a safiyar ranar Litinin, 5 ga watan Oktoba, 2020.

Dazu ne a hedikwatar hukumar NPC, Dr. Eyitayo Oyetunji ya yi wa manema labarai bayanin inda aka kwana game da aikin sharar fagen kidayar da za ayi.

“Shugaban kasa ya bada umarnin a sa Naira biliyan 4.5 a cikin kasafin kudin 2021 domin kammala wannan aiki a shirin kidayar da za ayi.” Inji Oyetunji.

KU KARANTA: Mashahuran da su ka halarci daurin Auren Aliyu Atiku da Fatima Ribadu

Shugaba Buhari ya ware N10b domin a kidaya yawan mutanen Najeriya
Shugaba Buhari Hoto: Channels TV
Asali: UGC

“Babu shakka wannan gagarumar nasara ce da aka samu a gwamnatin shugaba Buhari, ta fahimci amfanin alkaluma, musamman adadin ‘yan kasa.”

Ya ce adadin yawan ‘yan Najeriya ya na da muhimmanci wajen tsare-tsare da kason arzikin kasa.

Dazu mun kawo maku karin bayanai game da abin da ya sa duka Jihohi su ka maka Shugaban kasa a kotu, su na kukan Buhari ya toye masu hakkinsu.

Wasu Lauyoyi sun bayyana makasudin da ya sa Gwamnoni su ka yi wa Buhari fito-na-fito.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel