Bidiyo: Abubuwan al'ajabi da baku sani ba game da Shugaba Buhari

Bidiyo: Abubuwan al'ajabi da baku sani ba game da Shugaba Buhari

- Ko a cikin sa'oinsa, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi zarra kuma ya tsaya ba kamar sauran ba

- Ya yi shugaban kasa a zamanin mulkin sojoji, shugaban PTF da kuma shugaban kasa na farar hula

- Shugaban kasa Muhammadu Buhari yana da abubuwa masu tarin al'ajibi a tattare da shi

A duk lokacin da aka fara magana a kan tarihin Najeriya, dole ne a kira sunan shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Hakan ta kasance ne sakamakon rawar da ya taka a wasu muhimman abubuwan da suka faru kuma suka sauya akalar kasar nan baki daya.

Daga zamansa shugaban kasa a yayin mulkin soja har zuwa rike shugabancin PTF da yayi, da kuma zamansa shugaban kasa a karkashin mulkin fara hula.

Dole a ce shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi zarra cikin sa'o'insa da kuma sauran takwarorinsa a duniya.

Ga bidiyon wasu abubuwan al'ajabi da baku sani ba game da shugaban kasa Muhammadu Buhari.

KU KARANTA: Fyade: Kotu ta kori soja daga aiki, ta yanke masa hukuncin shekaru 5 a gidan yari

Bidiyo: Abubuwan al'ajabi da baku sani ba game da Shugaba Buhari
Bidiyo: Abubuwan al'ajabi da baku sani ba game da Shugaba Buhari. Hoto daga Vanguard
Asali: UGC

KU KARANTA: Da asusun bankunan fastoci muke amfani don guje wa jami'an tsaro - Dan damfarar yanar gizo

A wani labari na daban, a ranar Alhamis, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tabbatar da cewa kasar nan tana cikin mawuyacin hali a fannin tattalin arziki.

Ya ce hakan kuwa daidai yake da kowacce kasa domin kuwa dukkan duniya ne ake cikin wannan halin.

Buhari ya sanar da hakan ne a jawabinsa ga 'yan Najeriya a ranar da kasar ta cika shekaru 60 da samun 'yancin kai. Shugaban kasar ya kara da amincewa da cewa, kasar na fuskantar matsalolin tsaro daban-daban a sassan kasar.

Ya ce, "A yau na tabbatar da cewa Najeriya tana cikin mawuyacin hali na tattalin azriki kuma hakan ce ta kasance ga kowacce kasa a fadin duniya. Muna fuskantar kalubalen tsaro a sassa daban-daban na kasar nan."

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Khalid avatar

Aisha Khalid (Hausa editor) Aisha Khalid marubuciyar jaridar Legit.ng ce mai fatan shahara. Ta samu digirinta na farko a jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria a shekarar 2018. Ta kwashe shekaru tana rubutu a fannonin siyasa, nishadi, tsegumi da sauransu. Za a iya tuntubar ta a adireshin email din ta kamar haka: aisha.khaleed@corp.legit.ng