Rikicin APC a Ekiti: El-Rufai, Wase da Okorocha sun jagoranci kwamitin sulhu

Rikicin APC a Ekiti: El-Rufai, Wase da Okorocha sun jagoranci kwamitin sulhu

- Kwamitin kwantar da rikici jam'iyyar APC ta wakilta mutane 6 suje sasanci a jihar Ekiti

- Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ne ya jagoranci yan kwamitin kwantar da rikici

- Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ne Shugaban kwamitin, kuma ana rokon hadin kan yan jam'iyya

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya jagoranci kwamitin kwantar da rikicin jam'iyyar APC.

Inda ya shiga cikin mutum 6 da aka zaba wurin kwantar da rikici da ta taso a jihar Ekiti. Malam Nasir Ahmad El-Rufai ne shugaban kwamitin, Channels Tv ta wallafa.

An bayyanar da hakan a wata takarda da sakataren jam'iyyar, Yekini Nabena yasa hannu a kai ranar Talata.

Ya kara da cewa, Sanata John James Akpanudoedehe, ya rantsar da kwamitin kula da jam'iyyar APC da kwantar da rikici a babban ofishin jam'iyyar dake Abuja, kuma ya roki yan jam'iyyar su basu hadin kai.

A yadda takardar tazo, "Kamar yadda kwamitin kwantar da tarzomar jam'iyyar APC ta tanadar, muna rokonku da ku bada cikakken hadin kai don kwantar da duk wata rikici da fadace-fadacen da ke tsakanin yan jam'iyyar mu.

"Muna kira ga yan jam'iyya da kuma shugabannin jihar Ekiti da su hada kai da Gwamna Nasir El-Rufai wurin kwantar da rikicin da ta kunno kai a jihar Ekiti."

KU KARANTA: Durkusawar budurwa a gaban saurayi don karbar tayin aure ya janye cece-kuce

Rikicin APC a Ekiti: El-Rufai, Wase da Okorocha sun jagoranci kwamitin sulhu
Rikicin APC a Ekiti: El-Rufai, Wase da Okorocha sun jagoranci kwamitin sulhu. Hoto daga Channels TV
Source: Twitter

KU KARANTA: Ba dai a ma'aikata ta ba: Sadiya Farouq ta yi martani a kan ikirarin ICPC

A wani labari na daban, Shugaban kasa Muhammadu Buhari yace yana fatan babu wani dan Najeriya da zai wahala koda a wacce jam'iyya yake.

Shugaban kasar ya fadi hakan ne lokacin da Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya raka mataimakinsa, Philip Shuaibu da wasu yan jam'iyyarsu don godiya ga shugaban kasar a Abuja.

Shugaba Buhari ya sha alwashin kokarta wa wurin ciyar da al'umma gaba a bisa gaskiya da amana. Sannan ya roki jama'a dasu dage wurin bada hadin kai ga gwamnati don samun cigaban kasa.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng