'Yan bindiga sun afka wa mutane a Wasagu, sun kashe guda sun raunata da dama

'Yan bindiga sun afka wa mutane a Wasagu, sun kashe guda sun raunata da dama

- Ƴan bindiga sun kai hari a garin Wasugu da ke ƙaramar hukumar Wasagu Danko na jihar Kebbi

- Sun kashe mutum ɗaya, sun raunata raunata uku sun kuma yi awon gaba da wasu

- Kawo yanzu ƴan bindigan ba su tuntuɓi iyalan wadanda suka sace ba domin neman biyan kuɗin fansa

An kashe mutum ɗaya an kuma yi garkuwa da wasu bakwai a lokacin da ƴan bindiga suka kai hari garin Wasagu da ke ƙaramar hukumar Danko Wasagu na jihar Kebbi.

'Yan bindiga sun afka wa mutane a Wasagu, sun kashe guda sun raunata da dama
'Yan bindiga sun afka wa mutane a Wasagu, sun kashe guda sun raunata da dama. Hoto: @SaharaReporters
Source: Twitter

Yan bindigan sun afka garin na Wasugu a daren ranar Lahadi inda suka rika buɗe wa gidaje da mutane wuta.

Wani ganau, da ya yi magana da SaharaReporters ya ce mutum uku sun jikkata sakamakon harin.

DUBA WANNAN: Wasu jiga-jigan jam'iyyar APC sun marawa Obaseki baya saboda 2023 - Kakakin Tinubu

"Sun afka garin misalin ƙarfe 7 na dare suka fara harbe-harbe, mutum uku sun samu munanan rauni.

"Ɗaya daga cikin mutane ukun ya mutu yayin da sauran biyun sunan can suna karɓar magani a Cibiyar Lafiya ta Wasugu.

"Yan bindigan sun yi awon gaba da wasu mutane a garin mu yayin da wasu suka ruga gidajensu suka rufe kofofi.

"Bayan harin, mun gano cewa sun sace mutane biyar," a cewar wani mazaunin garin Aliyu.

KU KARANTA: 'Yan sintiri ga FG: A shirye muke mu kawar da 'yan ta'adda da 'yan bindiga

Ya ce duk da cewa a yanzu an samu lafiya a garin, mutane da dama suna zaman fargaba ne.

Ya ƙara da cewa har yanzu ƴan bindigan ba su tuntuɓi iyalan wadanda suka sace ba kan batun biyan kudin fansa.

A wani labarin daban da Legit.ng ta wallafa, mutane da dama sun bace sakamakon fadawa cikin rafin Epe da wata mota ta yi daga gadar Berger a jihar Legas.

The Punch ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a daren ranar Juma'a 25 ga watan Satumban 2020.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164