Majalisar Dinkin Duniya na son a yafe wa wanda ya yi batanci ga Annabi a Kano

Majalisar Dinkin Duniya na son a yafe wa wanda ya yi batanci ga Annabi a Kano

- Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci Nigeria da ta yafewa mawakin da aka yankewa hukuncin kisa saboda zarginsa da batanci ga Annabi Muhammad (SAW)

- Majalisar ta ce yin waka ba laifi bane, don haka, yanke hukuncin kisan ya sabawa dokar yancin dan Adam ta kasa da kasa

- Banda Yahaya Aminu Sharif, akwai kotun da ta yankewa wani dan shekaru 13 hukuncin shekaru 10 a gidan kaso, bisa zarginsa da batanci ga Annabi

A ranar Litinin, kwararru a Majalisar Dinkin Duniya sun bukaci Nigeria da ta saki mawakin da aka yankewa hukuncin kisa saboda zarginsa da batanci ga Annabi Muhammad (SAW).

A watan da ya gabata ne wata kotun shari'a a Kano, ta yankewa Yahaya Aminu Sharif hukuncin kisa, bayan da ya yi wakar batanci ga Musulunci da Annabi, kuma ya raba a WhatsApp.

A cikin wata sanarwar hadin guiwa daga kwararrun MDD, sun bayyana cewa "Waka ba laifi bace," kuma suka bayyana cewa tun farko mawakin bai samu kwararrun lauyoyi ba ne.

KARANTA WANNAN: APC ta yi babban rashi a jihar Delta, tsohon gwamna ya koma PDP

Majalisar Dinkin Duniya na son a yafe wa wanda da ya yi batanci ga Annabi a Kano
Majalisar Dinkin Duniya na son a yafe wa wanda da ya yi batanci ga Annabi a Kano - @bbchausa
Source: Twitter

Ita ma wata kwararra a hakkokin al'adun bil Adama, Karima Bennoune, ta bayyana cewa, sabawa dokar yancin dan Adam ne yanke hukuncin kisa don an yi waka tare da raba ta a kafofin sadarwa.

Ta roki Nigeria da ta janye wannan hukuncin kisan, kana ta tabbatar da tsaron lafiyar mawakin har zuwa lokacin da zai daukaka kara kan hukuncin.

KARANTA WANNAN: Gwamnatin Nigeria ta samu umurnin dakatar da yajin aikin NLC daga kotu

Fusatattun mutane sun gudanar da zanga zanga bayan da Sherif ya yi wakar, inda suka kona gidan iyayensa a ranar 4 ga watan Maris.

Bangaren shari'a na Nigeria na ci gaba da fuskantar suka tun bayan da ta yankewa dan shekaru 13 hukuncin shekaru 10 a gidan kaso, bisa zarginsa da batanci ga Annabi a wata muhawara.

Shi ma Daraktan kula da gidan tarihin Auschwitz, Omar Farouq, ya bukaci Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yafe wa yaron da ya yi batanci ga addini a Kano.

A wani labari, Gwamnan jihar Kaduna, Nasiru Elrufai ya musanta labarin da ake yadawa a kafafen watsa labarai na cewar ya karbi sunaye daga masu zaben sarkin Zazzau.

A cewar gwamnan, wannan labarin kanzon kurege ne kawai, kasancewar har yanzu, babu wani suna da ya zo gabansa, da sunan tantancewa don nada sabon sarki.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng