Gurfanar Obasanjo a gaban tsoho mai shekaru 94 ya janyo cece-kuce

Gurfanar Obasanjo a gaban tsoho mai shekaru 94 ya janyo cece-kuce

- Hoton tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya jawo cece-kuce a lokacin da aka ganshi yana nuna matukar girmamawa ga Pa Reuben Fasoranti a Akure

- Mai daukar hoto ya dauki hoton daidai lokacin da Obasanjo ya gurfana a gaban tsohon, lokacin da yakai mishi ziyara

- Pa yana zaune a kan kujera yana murmushi, yayin da tsohon shugaban kasar yake zaune a kasa sanye da kayansa na gargajiya

Wani hoto ya bayyana wanda ya nuna tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo a Akure, jihar Ondo, da Pa Reuben Fasoranti, wanda shekarar haihuwarsa bata dade da zagayowa ba.

Ba hoton ne abin bada labari ba, abin da tsohon shugaban kasar yayi a cikin hoton shine yafi zama abin bada labari.

Don girmama tsohon mai shekaru 94 da haihuwa, Pa Reuben Fasoranti, dattijon da Obasanjo ya kaiwa ziyara, tsohon shugaban kasar ya zauna a kasa.

Hakika, halin Obasanjo na ba wa manya girma, abin yabo ne da burgewa. Sannan duk inda yake, sai ya nishadantar da mutane.

A wani hoto da jaridar PM News suka wallafa, tsohon shugaban kasar yana zaune a kasa, yana murmushi da hularsa ta Yarabawa a kansa.

Kamar yadda aka dauki hoton tsohon mai shekaru 94 da haihuwa yana zaune akan kujera. Obasanjo na zaune kasa tare da Basorun Seinde Arogbofa.

KU KARANTA: Kyakyawar budurwa ta sha kunya, ta ce tana son saurayi amma yace ta cigaba da nema

Gurfanar Obasanjo a gaban tsoho mai shekaru 94 ya janyo cece-kuce
Gurfanar Obasanjo a gaban tsoho mai shekaru 94 ya janyo cece-kuce. Hoto daga PM News
Source: UGC

KU KARANTA: Dirarriyar budurwa ta wallafa hotunanta, ta bukaci duk saurayin da ke da bukata ya nemi soyayyarta

A wani labari na daban, Shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Juma'a, 25 ga watan Satumba, ya ce ya dauka alhakin lallasa APC da aka yi a zaben ranar Asabar da ta gabata na gwamnoni.

Shugaban kasar ya sanar da hakan a gidan gwamnati bayan karbar sabon gwamna jihar Edo, Godwin Obaseki, tare da mataimakinsa Philip Shaibu da wasu jiga-jigan jam'iyyar PDP.

Buhari ya ce a matsayinsa na babban jiigo a jam'iyyarsa, shine yakamata a dora wa laifin komai ballantan a lokacin da aka lallasa su a zabe.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng