An yi garkuwa da jigon jam'iyyar PDP a Katsina

An yi garkuwa da jigon jam'iyyar PDP a Katsina

- 'Yan bindiga sun sace tsohon shugaban matasa na jam'iyyar Peoples Democratic Party, PDP a Katsina, Alhaji Ali Sukuntuni

- Rahotanni sun bayyana cewa 'yan bindigan sun afka garin ne a safiyar ranar Alhamis suka kuma yi awon gaba da shi

- A ranar Laraba 'yan bindiga sun kuma yi garkuwa da 'yar uwar shugaban wani bankin gwamnatin tarayya, Asiya Musa Dangiwa

An yi garkuwa da jigon jam'iyyar PDP a Katsina
An yi garkuwa da jigon jam'iyyar PDP a Katsina. Hoto @MobilePunchng
Source: Twitter

KU KARANTA: Borno: An sun kashe manyan kwamandojin 'yan Boko Haram 7 a Tafkin Chadi

Wasu miyagu da ake zargin 'yan bindiga dadi ne sun yi garkuwa da Alhaji Ali Sukuntuni, jigo a jam'iyyar Peoples Democratic Party, PDP, a garin Rimaye da ke karamar hukumar Kankia na jihar Katsina.

'Yan bindigan sun afka wa garin ne a safiyar ranar Alhami kamar yadda Sahara Reporters ta ruwaito.

Sukuntuni shine tsohon shugaban matasa na jam'iyyar PDP a karamar hukumar.

Ana dai cigaba da garkuwa da mutane da kuma kai hare hare a sassan arewacin Najeriya duk da karin jami'an tsaro da aka tura a yankin.

DUBA WANNAN: Dalilin da yasa 'yan Najeriya ke korafi kan karin kudin wutar lantarki - Sanusi II

Idan za a iya tunawa masu garkuwa da mutanen a ranar Laraba sun sace 'yar uwar shugaban wani bankin gwamnatin tarayya a jihar, Asiya Musa Dangiwa.

Thisday ta ruwaito cewa wadanda suka sace Ali sun afka gidansa ne a daren ranar Laraba bayan ya dawo daga unguwa suka bincike gidansa sannan suka yi awon gaba da shi zuwa wani wurin da ba a sani ba.

Wata majiya daga garin ta bayyana cewa masu garkuwa da mutanen da adadinsu ya kai shida sun shigo garin ne a kan babura suka shiga gidansa suka tafi da shi har kuma yanzu ba su tuntubi iyalansa ba.

Da aka tuntube shi, Kakakin 'yan sandan jihar, Gambo Isah ya ce: "Eh, da gaske ne. Na kira DPO ya tabbatar min da afkuwar abin kuma muna kokarin ceto shi."

A wani rahoton, kun ji Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna, NAFDAC, ta rufe kamfanonin kera magungunan dabobi na jabu a karamar hukumar Bichi na jihar Kano.

Shugaban hukumar na jihar, Shaba Muhammad ne ya bayyana hakan yayin wata sumame da jami'an hukumar suka kai Laraba a Bichi kamar yadda Daily Nigerian ta ruwaito.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164