Yanzu yanzu: Allah ya yiwa Sarkin Biu, Mai Umar, rasuwa

Yanzu yanzu: Allah ya yiwa Sarkin Biu, Mai Umar, rasuwa

- Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un

- Cikin shekarar nan, jihar Borno ta sake rashin wani Basarake

- Alhaji Mai Umar ya yi shekaru 31 kan karagar mulkin masarautar Biu kafin rasuwarwa

Allah ya yiwa mai martaba Sarkin masarautar Biu a jihar Borno , Alhaji Mai Umar Mustapha Aliyu, rasuwa yana mai shekaru 79.

Ya rasu a daren Litinin a asibitin gwamnatin tarayya dake Gombe, bayan gajeruwar rashin lafiya.

A cewar Iyalan marigayin, sun bayyana cewa: "Mun yi rashin ginshikin masarrautar Biu da jihar Borno gaba daya, Sarkin Biu.”

”Allah ya gafarta kura-kuransa kuma ya azurtashi da gidan Aljannah Firdawsi mafi girma.”

Alhaji Mai Umar Mustapha Aliyu ya hau mulkin masarautar ne a shekarar 1989.

KU KARANTA WANNAN: Shagalin bikin nadin sarautar sabon Sarkin Bama (Hotuna)

Yanzu yanzu: Allah ya yiwa Sarkin Biu, Mai Umar, rasuwa
Yanzu yanzu: Allah ya yiwa Sarkin Biu, Mai Umar, rasuwa
Source: Twitter

Bayan rasuwar Shehun Bama, Alhaji Kyari El-Kanemi, Gwamna Babagana Zulum ya nada sabon sarki a Bama.

Amma a yau Asabar, 9 ga watan Mayun 2020 aka yi bikin nadin sarautar sabon sarkin Alhaji Umar Ibn Kyari El-Kanemi.

DUBA NAN: Zulum zai dauki ma'aikatan lafiya 594 a fadin jihar Borno

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng