An kama wani da ya dauki dan uwansa aiki ba bisa ka'ida ba a Niger

An kama wani da ya dauki dan uwansa aiki ba bisa ka'ida ba a Niger

- An kama wani mutum da ke aiki a ma'aikatar lafiya ta jihar Niger da ya ɗauki ɗan uwansa aiki ba bisa ka'ida ba

- Kwamishinan ƴan sandan jihar ya ce kwamitin tantance ma'aikata ta gano badaƙalar ne yayin aikinta

- An gano cewa mutum ya ɗauki ɗan uwansa aikin ne tun a 2009 a kan mataki na 11 duk da bashi da takardu yanzu har ya kai mataki na 14

Ƴan Sanda a jihar Niger sun kama yaya da ƙani da ake zargi da hannu cikin damfarar daukan aiki a ma'aikatar lafiya ta jihar.

Kwamishinan ƴan sandan jihar, Mista Adamu Usman ya shaidawa manema labarai a Minna a ranar Talata cewa an gano badaƙalar ne yayin aikin tantance ma'aikata a jihar.

An kama wani da ya dauki dan uwansa aiki ba bisa kaida ba a Niger
An kama wani da ya dauki dan uwansa aiki ba bisa kaida ba a Niger
Asali: Twitter

Ya ce kwamitin binciken ta gano cewa wani ma'aikacin hukumar ya saka sunan ɗan uwansa a jerin sunayen waɗanda gwamnatin jihar zata ɗauka aiki a jihar.

A cewar kwamishinan ƴan sandan, an gano cewa an ɗauki daya daga cikin ƴan uwan aiki a gwamnatin jihar a matsayi ta 11 ba tare da ya mallaki takardun da ake bukata ba.

DUBA WANNAN: Kudancin Kaduna: Mabiya sun ce fasto ya siyo bindigu da kudin baikonsu

Usman ya ce kwamitin ta gano wani daga cikin ma'aikacin ta a ma'aikatar lafiya ya ɗauki ɗan uwansa mai sana'ar achaɓa aiki ba tare da ya mallaki takardun da suka cancanta ba tun a 2009.

"Mohammed Ndanusa ya amsa cewa ya aikata laifin inda ya ce ya ɗauki ɗan uwansa aiki a mataki ta 11 a 2009 kuma ya yi ta yi masa ƙarin girma zuwa matakinsa na yanzu na 14"

Kwamishinan ƴan sandan ya ce za a gurfanar da wanda ake zargin a kotu da zarar an kammala bincike.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164