An kama wani da ya dauki dan uwansa aiki ba bisa ka'ida ba a Niger

An kama wani da ya dauki dan uwansa aiki ba bisa ka'ida ba a Niger

- An kama wani mutum da ke aiki a ma'aikatar lafiya ta jihar Niger da ya ɗauki ɗan uwansa aiki ba bisa ka'ida ba

- Kwamishinan ƴan sandan jihar ya ce kwamitin tantance ma'aikata ta gano badaƙalar ne yayin aikinta

- An gano cewa mutum ya ɗauki ɗan uwansa aikin ne tun a 2009 a kan mataki na 11 duk da bashi da takardu yanzu har ya kai mataki na 14

Ƴan Sanda a jihar Niger sun kama yaya da ƙani da ake zargi da hannu cikin damfarar daukan aiki a ma'aikatar lafiya ta jihar.

Kwamishinan ƴan sandan jihar, Mista Adamu Usman ya shaidawa manema labarai a Minna a ranar Talata cewa an gano badaƙalar ne yayin aikin tantance ma'aikata a jihar.

An kama wani da ya dauki dan uwansa aiki ba bisa kaida ba a Niger
An kama wani da ya dauki dan uwansa aiki ba bisa kaida ba a Niger
Asali: Twitter

Ya ce kwamitin binciken ta gano cewa wani ma'aikacin hukumar ya saka sunan ɗan uwansa a jerin sunayen waɗanda gwamnatin jihar zata ɗauka aiki a jihar.

A cewar kwamishinan ƴan sandan, an gano cewa an ɗauki daya daga cikin ƴan uwan aiki a gwamnatin jihar a matsayi ta 11 ba tare da ya mallaki takardun da ake bukata ba.

DUBA WANNAN: Kudancin Kaduna: Mabiya sun ce fasto ya siyo bindigu da kudin baikonsu

Usman ya ce kwamitin ta gano wani daga cikin ma'aikacin ta a ma'aikatar lafiya ya ɗauki ɗan uwansa mai sana'ar achaɓa aiki ba tare da ya mallaki takardun da suka cancanta ba tun a 2009.

"Mohammed Ndanusa ya amsa cewa ya aikata laifin inda ya ce ya ɗauki ɗan uwansa aiki a mataki ta 11 a 2009 kuma ya yi ta yi masa ƙarin girma zuwa matakinsa na yanzu na 14"

Kwamishinan ƴan sandan ya ce za a gurfanar da wanda ake zargin a kotu da zarar an kammala bincike.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel