Dangote ya bukaci a bawa Okonjo Iweala babban mukami a WTO

Dangote ya bukaci a bawa Okonjo Iweala babban mukami a WTO

- Ngozi Okonjo-Iweala na ta samun goyon baya daga sassa daban-daban a kokarin da take na zama darakta janar a kamfanin kasuwanci na duniya

- Kwanan nan, tsohuwar ministar kudin ta Najeriya ta samu goyon bayan Aliko Dangote wajen samun wannan mukami

- Fitaccen dan kasuwar ya bayyana cewa WTO na bukatar Iweala a matsayin jigo wajen kasuwanci a duniya

Aliko Dangote, daya daga cikin manyan masu kudin nahiyar Africa, ya nuna goyon bayansa ga tsohuwar ministar kudi, Ngozi Okonjo-Iweala, a matsayin wacce ta dace ta rike mukamin darakta janar ta kamfanin kasuwanci na duniya.

Dangote ya bayyana cewa kamfanin na bukatar wacce keda kwarewa ta kowanne fanni na kasuwanci a duniya kamar Okonjo-Iweala a matsayin jagora.

Fitaccen mai kudin na Afrika ya nuna goyon bayansa ne a shafinsa na Twitter a ranar Talata, 1 ga watan Satumba.

KU KARANTA: Bude makarantu: Gwamnatin tarayya ta gargadi jihohin da suke shirin bude makarantu a Najeriya

Dangote ya ce: "A wannan lokaci da muke ciki, WTO tana bukatar mutum mai kwarewa kamar Dr Ngozi Okonjo Iweala ta jagoranci kamfanin a wannan lokaci da ake ta fama da matsaloli iri-iri.

"Na zabe ta a kowanne mataki. Ina goyon bayanta dari bisa dari ta jagoranci WTO."

Dangote ya bukaci a bawa Okonjo Iweala babban mukami a WTO
Dangote ya bukaci a bawa Okonjo Iweala babban mukami a WTO
Asali: UGC

Fitaccen dan yankin arewan ya bayyana cewa tunda har Okonjo Iweala ta gano matsalolin da ake samu a fannin kasuwanci na duniya, za ta iya kawo karshen duka matsalolin.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng