Dangote ya bukaci a bawa Okonjo Iweala babban mukami a WTO
- Ngozi Okonjo-Iweala na ta samun goyon baya daga sassa daban-daban a kokarin da take na zama darakta janar a kamfanin kasuwanci na duniya
- Kwanan nan, tsohuwar ministar kudin ta Najeriya ta samu goyon bayan Aliko Dangote wajen samun wannan mukami
- Fitaccen dan kasuwar ya bayyana cewa WTO na bukatar Iweala a matsayin jigo wajen kasuwanci a duniya
Aliko Dangote, daya daga cikin manyan masu kudin nahiyar Africa, ya nuna goyon bayansa ga tsohuwar ministar kudi, Ngozi Okonjo-Iweala, a matsayin wacce ta dace ta rike mukamin darakta janar ta kamfanin kasuwanci na duniya.
Dangote ya bayyana cewa kamfanin na bukatar wacce keda kwarewa ta kowanne fanni na kasuwanci a duniya kamar Okonjo-Iweala a matsayin jagora.
Fitaccen mai kudin na Afrika ya nuna goyon bayansa ne a shafinsa na Twitter a ranar Talata, 1 ga watan Satumba.
KU KARANTA: Bude makarantu: Gwamnatin tarayya ta gargadi jihohin da suke shirin bude makarantu a Najeriya
Dangote ya ce: "A wannan lokaci da muke ciki, WTO tana bukatar mutum mai kwarewa kamar Dr Ngozi Okonjo Iweala ta jagoranci kamfanin a wannan lokaci da ake ta fama da matsaloli iri-iri.
"Na zabe ta a kowanne mataki. Ina goyon bayanta dari bisa dari ta jagoranci WTO."

Asali: UGC
Fitaccen dan yankin arewan ya bayyana cewa tunda har Okonjo Iweala ta gano matsalolin da ake samu a fannin kasuwanci na duniya, za ta iya kawo karshen duka matsalolin.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng