Zaben Ondo: Dan takarar gwamna karkashin jam'iyyar PDP ya zabi abokin takararsa

Zaben Ondo: Dan takarar gwamna karkashin jam'iyyar PDP ya zabi abokin takararsa

- Mr Eyitayo Jegede ya zabi Hon. Ikengboju Gboluga a matsayin abokin takararsa

- Mr Jegede shine dan takarar gwamnan jihar Ondo a karkashin jam'iyyar PDP

- Za a gudanar da zaben gwamnan jihar Ondo ne a ranar 10 ga watan Oktoba, 2020

Dan takarar gwamnan jihar Ondo a karkashin jam'iyyar PDP, Eyitayo Jegede ya zabi Hon. Ikengboju Gboluga a matsayin abokin takararsa.

Mr. Jegede ya sanar a hakan a shafinsa na Twitter a ranar Talata.

"Ina mai farin cikin sanar da ku cewa Hon. Ikengboju Gboluga zai yi takara tare dani a babban zaben jihar da za a gudanar ranar 10 ga watan Oktoba 2020," a cewarsa.

Hon. Gboluga ya kasance mamba ne a majalisar wakilan tarayya da ke wakiltar mazabar Okitipupa/Irele a majalisar tarayya.

Wannan na zuwa awanni 24 bayan da dan takarar jam'iyyar Zenith Labour Party (ZLP) a jihar Ondo, Agboola Ajayi, ya zabi nasa abokin takarar don fuskantar zaben jihar.

KARANTA WANNAN: Gwamnatin tarayya ta magantu kan ranar bude jami'o'i

Zaben Ondo: Dan takarar gwamna karkashin jam'iyyar PDP ya zabi abokin takararsa
Zaben Ondo: Dan takarar gwamna karkashin jam'iyyar PDP ya zabi abokin takararsa
Asali: Twitter

Ajayi wanda ya kasance mataimakin gwamnan jihar ya zabi Gboye Adegbenro a matsayin abokin takararsa.

Mataimakin gwamnan, a makon da ya gabata ne ya fice daga jam'iyyar PDP zuwa jam'iyyar ZLP a Akure, babban birnin jihar.

A wani labarin; Gwamnatin tarayya ta ba kungiyar dalibai ta kasa (NANS) tabbacin cewa za a bude makarantu da suka hada da jami'o'i da zan an samu damar yin hakan.

Shugaban kwamitin yaki da COVID-19 na kasa kuma sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha ya bada tabbacin a wani taron bita na kwamitin a ranar Litinin.

Ya ce a ranar Litinin dalibai suka fara zana jabawarar kammala makarantar sakandire, kuma kwamitin PTF na farin ciki na yadda makarantun suke kiyaye dokoki.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng