Da duminsa: Sabbin yan Najeriya 329 sun kamu da Coronavirus

Da duminsa: Sabbin yan Najeriya 329 sun kamu da Coronavirus

Hukumar Takaita Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 329 a fadin Najeriya yau Juma'a.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:49 na daren ranar Juma'a 14 ga Agustan shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta a shafinta na Twitter, ta bayyana adadin wadanda suka kamu da cutar a jihohin Najeriya kamar haka:

Lagos-113

Kaduna-49

FCT-33

Plateau-24

Kano-16

DUBA WANNAN: Buhari ya yi ta'aziyar rasuwar Walter Carrington

Edo-15

Ogun-14

Delta-13

Osun-10

Oyo-8

Ekiti-6

Bayelsa-6

Akwa Ibom-5

Borno-4

Enugu-4

Ebonyi-3

Rivers-2

Bauchi-1

Nasarawa-1

Gombe-1

Niger-1

Alkalluman da hukumar ta dakile cututtukan ta fitar a ranar Juma'a 14 ga Agustan shekarar 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu da cutar ta korona a Najeriya ya kai 48,445 .

An sallami mutum 35,998 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta kashe jimillar mutane 973.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164