Da duminsa: Sabbin yan Najeriya 329 sun kamu da Coronavirus

Da duminsa: Sabbin yan Najeriya 329 sun kamu da Coronavirus

Hukumar Takaita Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 329 a fadin Najeriya yau Juma'a.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:49 na daren ranar Juma'a 14 ga Agustan shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta a shafinta na Twitter, ta bayyana adadin wadanda suka kamu da cutar a jihohin Najeriya kamar haka:

Lagos-113

Kaduna-49

FCT-33

Plateau-24

Kano-16

DUBA WANNAN: Buhari ya yi ta'aziyar rasuwar Walter Carrington

Edo-15

Ogun-14

Delta-13

Osun-10

Oyo-8

Ekiti-6

Bayelsa-6

Akwa Ibom-5

Borno-4

Enugu-4

Ebonyi-3

Rivers-2

Bauchi-1

Nasarawa-1

Gombe-1

Niger-1

Alkalluman da hukumar ta dakile cututtukan ta fitar a ranar Juma'a 14 ga Agustan shekarar 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu da cutar ta korona a Najeriya ya kai 48,445 .

An sallami mutum 35,998 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta kashe jimillar mutane 973.

Asali: Legit.ng

Online view pixel