Da dumi-dumi: Kungiyar Barcelona ta lallasu 8-2, lallasuwa mafi muni cikin sama da shekaru 70

Da dumi-dumi: Kungiyar Barcelona ta lallasu 8-2, lallasuwa mafi muni cikin sama da shekaru 70

Kungiyar kwallon Bayern Munich ta ci mutuncin kungiyar Barcelona da ci 8 ga 2 a wasan zarcewa kusa na da na karshe ana gasar Zakarun Turai da aka buga yau Juma'a a a birnin Lison, kasar Portugal.

Thomas Muller da Phillipe Coutinho sun samu zura kwalle biyu-biyu inda suka karya lagwon Barcelona da yiwuwar cigaba da zaman Messi a kungiyar.

Yanzu Bayern Munich za ta kara da duk wanda yayi nasara tsakanin Manchester City da Lyon gobe.

Wadanda suka zuka kwallo wa Bayern Munich sune: Thomas Muller (2), Joshua Kimmich (1), Robert Lewandowski (1), Philippe Coutinho (2), S Ganbry (1) da Ivan Preisic (1).

Na kungiyar Barca kuwa akwai Luis Suarez (1), sai David Alaba na Bayern Munich wanda ya ci gidansa.

Da dumi-dumi: Kungiyar Barcelona ta lallasu 8-2, lallasuwa mafi muni tun shekarar 1940
Da dumi-dumi: Kungiyar Barcelona ta lallasu 8-2, lallasuwa mafi muni tun shekarar 1940
Asali: Getty Images

Mun kawo muku rahoton cewa Mai tsaron bayan kungiyar kwallon Barcelona, Samuel Umtiti, ya kamu da cutar Coronavirus.

Kungiyar kwallon ta bayyana cewa Dan kwallon wanda ya lashe kofin duniya a 2018, ya kamu da cutar ne a jawabin da ta saki ranar Juma'a.

Umititi, wanda yake jinya kuma ba zai yi wasa da yammacin nan ba a gasar zakarun Turai inda kungiyarsa Barcelona za ta goge raini da kungiyar kwallon Bayern Munich a birnin Lisbon, Portugal.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng