Adama Indimi da mijinta sun ziyarci surukinta a fadarsa da ke Kogi (Hotuna)

Adama Indimi da mijinta sun ziyarci surukinta a fadarsa da ke Kogi (Hotuna)

Adama Indimi da mijinta, Malik Ado-Ibrahim, sun kai wa surukinta, Ohinoyi na kasar Ebira, Alhaji (Dr) Ado Ibrahim, ziyara a fadarsa kwanaki kadan bayan daura aurensu a Maiduguri, jihar Borno.

Malik yarima ne na kasar Ebira a jihar Kogi.

An daura aurensu ne a ranar Asabar 8 ga watan Agustan shekarar 2020 misalin karfe 10 na safe.

Amma an fara bukukuwan daurin auren tun daren ranar Juma'a 7 ga watan Agusta a Maiduguri.

Malik Ado Ibrahim, shine wanda ya kafa kamfanin Bicernergy

Adama da Malik sun yi soyaya na kimanin shekara daya sannan suka yanke shawarar yin aure a ranar 8 ga watan Agustan shekarar 2020.

Ga wasu hotuna daga ziyarar da suka kai wa sarkin na kasar Ebira a kasa.

Adama Indimi da mijinta sun ziyarci surukinta a fadarsa (Hotuna)
Malik Ado Ibrahim da amaryarsa, Adama Indimi a fadar Ohinoyi na Igbira, Alhaji Dr Ado Ibrahim. Hoto daga LIB
Asali: Twitter

Adama Indimi da mijinta sun ziyarci surukinta a fadarsa (Hotuna)
Adama Indimi da surukinta mai marta Alhaji Dr Ado Ibrahim a fadarsa. Hoto daga LIB
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: Yadda wani masanin magunguna ya mutu yayin gasar lalata da karuwa a otel

Adama Indimi da mijinta sun ziyarci surukinta a fadarsa (Hotuna)
Adama Indimi ta ziyarci surukinta a fadarsa da ke jihar Kogi. Hoto daga LIB
Asali: Twitter

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164