Ana sauran yan makonni daurin aurenta, babbar mota ta murkushe kyakkyawar budurwa

Ana sauran yan makonni daurin aurenta, babbar mota ta murkushe kyakkyawar budurwa

An tabbatar da mutuwar wata budurwa yar Najeriya mai suna, Immaculate Okuchu, bayan wata babbar mota ta murkushe ta a unguwar Ajah a jihar Legas.

The Nation ta ruwaito cewa budurwar na shirin aurenta da zai gudana a watan Oktoba, ta mutu sakamakon hadarin motan.

'Yar uwar magayiyar, Magdalene Okuchu, ta bayyana sakon jimaminta a shafinta na Facebook.

Tace: "Har yanzu na kasa yarda, yan awanni kina magana cikin farin ciki, har kika daura kayayyakinki a kafar sada zumunta. Da Allah ya hanaki zuwa aiki yau da baki fuskanci hadarin ba."

Ana sauran yan makonni daurin aurenta, babbar mota ta murkushe kyakkyawar budurwa
Ana sauran yan makonni daurin aurenta, babbar mota ta murkushe kyakkyawar budurwa
Asali: Instagram

KU KARANTA: Rabuwan kai tsakanin kabilar Igbo: Biyafara muke so, babu ruwanmu da kujeran shugaban kasa - Dattawan Biyafara

Tuni masu ta'azziya sun cika shafinta na Facebbok da sakonni.

Immaculate Okochu yar asalin Ebu a jihar Delta ce , kuma tana zama a Apapa, jihar Legas kafin mutuwarta.

Ta halarci makarantar sakandaren Ajeromi Ifelodun Senior High School da Kwalejin fasahar Yabatech.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng