Mutanen da cutar korona ta harba a Najeriya sun zarta 46,000 - NCDC

Mutanen da cutar korona ta harba a Najeriya sun zarta 46,000 - NCDC

Babu shakka hukumomin lafiya na ci gaba da aiki tukuru domin dakile yaduwar cutar korona a Najeriya, sai dai fa lamarin ya ci tura domin kuwa cutar na ci gaba da bazuwa babu sassauci.

A halin yanzu an samu bullar cutar covid-19 a duk jihohi 36 na Najeriya da kuma babban birnin tarayya kamar yadda alkaluman cibiyar dakile yaduwar cututtuka a kasar NCDC suka tabbatar.

Taskar bayanai ta NCDC a ranar Lahadi, 9 ga watan Agustan 2020, ta ce cutar corona ta harbi mutane 46,577 yayin da mutum 33,186 suka samu waraka.

Ya zuwa yanzu dai mutane 945 cutar ta hallaka a fadin Najeriya kamar yadda hukumar NCDC ta fidda bayanan alkalumanta.

Shugaban NCDC; Chikwe Ihekweazu
Shugaban NCDC; Chikwe Ihekweazu
Asali: Facebook

Rumbun tattaro bayanai na NCDC ya nuna cewa, an yi wa mutum 317,496 gwajin cutar a duk fadin kasar tun bayan bullarta karo na farko a ranar 27 ga watan Fabrairun 2020.

Haka kuma alkaluman cibiyar dakile cututtuka ta kasar sun nuna cewa, mutum 12,446 ne suka rage masu dauke da kwayoyin cutar.

KARANTA KUMA: Hadin gwiwar dakarun soji: Kwararre ya yi hasashen ta'addanci zai zamo tarihi a Najeriya ba jimawa

Da misalin karfe 11.17 na jiya Lahadi da daddare, NCDC ta sanar da cewa an gano karin sabbin mutane 437 da cutar ta harba a fadin Najeriya.

Sabbin mutane 437 da cutar ta harba cikin jihohi 17 sun kasance kamar haka:

Legas (107), Abuja (91), Filato (81), Kaduna (32), Ogun (30), Kwara (24), Ebonyi (19), Ekiti (17), Oyo (8), Borno (6), Edo (6), Kano (4), Nasarawa (3), Osun (3), Taraba (3), Gombe (2) da Bauchi (1).

Har kawo yanzu jihar Legas ce a kan sahu na gaba ta fuskar yawan mutanen da cutar ta harba, sai kuma birnin Abuja a mataki na biyu yayin da jihar Oyo ta biyo bayansu a mataki na uku.

Ga jerin adadin mutanen da cutar ta harba cikin kowace daya daga cikin jihohi 36 na Najeriya da cutar ta bulla:

Lagos - 15,875

Abuja - 4,467

Oyo - 2,868

Edo - 2,382

Ribas - 1,939

Kano - 1,626

Kaduna - 1,598

Delta - 1,596

Plateau - 1,502

Ogun - 1,469

Ondo - 1,284

Enugu - 905

Ebonyi - 870

Kwara - 857

Katsina - 746

Borno - 688

Abia - 644

Gombe - 631

Osun -628

Bauchi - 577

Imo - 476

Benue - 409

Nasarawa - 370

Bayelsa - 346

Jigawa - 322

Akwa Ibom - 235

Niger -226

Adamawa - 185

Ekiti - 178

Sokoto -154

Anambra -142

Kebbi - 90

Zamfara - 77

Taraba - 75

Kuros Riba - 68

Yobe - 67

Kogi - 5

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel