Obaseki ya aikata laifin da ya cancani a tsigeshi - Tinubu ya yi tsokaci

Obaseki ya aikata laifin da ya cancani a tsigeshi - Tinubu ya yi tsokaci

Babban jigon jam'iyyar All Progressives Congress (APC), Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya sanya albarkacin bakinsa cikin dambarwan siyasan dake gudana a majalisar dokokin jihar Edo.

Tinubu ya daura laifin dukkan abubuwan dake faruwa kan gwamna jihar, Godwin Obaseki, inda ya ce an ci mutuncin demokradiyya.

A jawabin da ya saki daren jiya, Tinubu ya ce tare kofar majalisa domin hana yan majalisa shiga a rantsar da su cin mutunci ne ga kundin tsarin mulki.

Ya bayyana cewa "Abubuwan da Gwamna Obaseki yayi a shekara daya da ya shude ko shakka babu ya cancanci a tsigeshi"

Ya kara da cewa duk da haka "wadannan yan majalisan basu yi barazanar tsigeshi ba. Kawai manufarsu ita ce su gudanar da ayyukansu kamar yadda al'ummarsu suka bukacesu."

A cewarshi, "Dalilin hana zababbun yan majalisan dokokin jihar Edo aikinsu da doka ta bukacesu, gwamna Obaseki ya yaudari al'ummar jiharsa kuma ya bayyana jahilcinsa ga kundin tsarin mulkin Najeriya a fili."

Ya ce a matsayin gwamna, ya kamata a ce Obaseki "ya sani fiye da gamarin mutane kafin hana majalisa dokokin jihar amma yana bukatan a koya masa darasi yanzu."

Obaseki ya aikata laifin da ya cancani a tsigeshi - Tinubu ya yi tsokaci
Obaseki ya aikata laifin da ya cancani a tsigeshi - Tinubu ya yi tsokaci
Asali: UGC

KU KARANTA: Bankin duniya ya amince da baiwa Najeriya $114.28m don yakar cutar Korona

A bangare guda, Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki, ya mayarwa gwamnan jihar Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje martani mai zafi don ya ce babu aikin a zo a ganin da yayiwa al'ummar Edo.

Yayinda yake magana a fadar shugaban kasa ranar Juma'a, Ganduje wanda shine shugaban kwamitin yakin neman zaben APC a jihar Edo ya ce gazawar Obaseki zai saukaka musu wajen samun nasara a zaben ranar 19 ga Satumba.

Amma martani kan jawabin Ganduje, mai magana da yawun Obaseki, Crusoe Osagie , ya ce Ganduje bai da alhakin auna kokarin Obaseki saboda "irin bidiyon da ya bayyana kansa yana cusa Dalan da ya karba daga yan kwangila."

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng