Katsina: Fargabar harin ƴan bindiga yasa an rufe jami'ar Tarayya ta Dutsin-Ma

Katsina: Fargabar harin ƴan bindiga yasa an rufe jami'ar Tarayya ta Dutsin-Ma

Shugaban Jami'ar Tarayya da ke Dutsin-Ma, Katsina, Farfesa Armaya'u Bichi, ya sanar da dakatar da duk ayyuka a mazaunin jami'ar na dindindin saboda fargabar hare-haren ƴan bindiga a ƙaramar hukumar.

Wannan umurnin na ƙunshe ne cikin wata sanarwa ta musamman mai ɗauke da sa hannun Direktan Hulda da Jama'a na Jami'ar, Habibu Matazu.

A cewar sanarwar, an umurci dukkan ma'aikatan jami'ar su dena zuwa mazaunin jami'ar na dindindin domin yin ayyuka a halin yanzu.

Jami'ar Tarayya da ke Dutsin-Ma, Katsina
Jami'ar Tarayya da ke Dutsin-Ma, Katsina. Hoto daga Daily Nigerian
Asali: Twitter

"Umurnin ya fito ne ta ofishin rajistara, Alh. Dalha Kankia bayan rahotannin hare-haren ƴan bindiga a ƙauyukan da ke makwabtaka da jami'ar.

"Hakan yasa shugaban jami'ar dukkan ma'aikatan jami'ar da ke gudanar da ayyuka su koma mazaunin jami'ar na wucin gadi daga ranar Alhamis 6 ga watan Agusta.

"Za a sanar da mutanen da ke jami'ar ranar da za a cigaba da ayyuka a mazaunin jami'ar ta dindindin, " a cewar sanarwar.

DUBA WANNAN: An kama dagajin ƙauye da ke haiƙe wa ƴarsa mai shekara 15

A baya, Legit.ng ta ruwaito cewa ana cigaba da kai hare hare a jihar a sassa daban daban.

A ranar Laraba, Gwamna Aminu Masari ya gana da Shugaba Muhammadu Buhari inda ya yi masa bayanin halin da jihar ke ciki.

Da ya ke zantawa da manema labarai a gidan gwamnati bayan ganawa da shugaban kasa, gwamnan ya ce ana iya ƙoƙarin ganin an magance ƴan bindigan amma suna yi wa shirin noma na gwamnati cikas.

"Tabbas, za a samu wasu matsaloli, saboda a jihar baki daya, rikicin ƴan bindigan ya shafi kananan hukumomi tara cikin 34," a cewar Masari.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164