COVID-19: Buhari ya sabunta dokar kulle da makonni hudu
Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta jinkirta sassauta dokar kulle na mataki na biyu na annobar korona da makonni hudu.
Wannan shine karo na uku da ake jinkirta sassauta dokar kullen na mataki na biyu kamar yadda The Nation ta ruwaito.
Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, kuma shugaban kwamitin shugaban kasa na yaki da COVID-19, Boss Mustaha ne ya sanar da hakan yayin jawabin da kwamitin ke yi a Abuja.

Asali: Twitter
DUBA WANNAN: Soja da ta yi ciki bayan ƴan bindiga sun mata fyade ta daukaka kara kan korarta daga aiki
Matakin ba zai rasa nasaba ba da yawaita sabbin mutane da ke kamuwa da cutar ta korona a baya bayan nan da kuma rashin bin dokokin kiyaye yaduwar cutar da SGF din ya ce jihohi ba su yi.
Hakan ne zuwa ne a lokacin da jihohin kasar ke shirin bude makarantun sakandare domin dalibai ajin karshe su rubuta jarabawar kammala karatu ta WAEC da JSCE.
Ku saurari cikaken rahoton ...
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng