Da duminsa: Shugaba Buhari ya nada AbdulMumini Jibrin wani babban mukami

Da duminsa: Shugaba Buhari ya nada AbdulMumini Jibrin wani babban mukami

- Tsohon dan majalisar wakilai, AbdulMumini Jibrin ya samu mukami daga shugaban kasa

- Jawabi daga hadimin gwamnan Kano ya nuna gwamna Ganduje yana tayashi murna

- Jibrin ya samu matsala da jam'iyyar APC a jihar Kano kuma hakan ya ja masa rasa kujeransa a majalisa

Shugaba Muhammadu Buhari ya nada tsohon dan majalisa, AbdulMumini Jibrin a matsayin sabon Diraktan hukumar gidajen tarayya (sashen cigaban kasuwanci, da samar da gidaje ga jama'a)

Hakan ya bayyana cewa a jawabin hadimin gwamna Abdullahi Ganduje kan labarai, Salihu Tanko Yakassai, ranar Laraba 5 ga Agusta, 2020.

Yakassai ya ce gwamnan ya taya Jibrin murna kan sabon matsayinsa kuma ya godewa shugaba Buhari bisa wannan amincewa da yayi da Jibrin.

Da duminsa: Shugaba Buhari ya nada AbdulMumini Jibrin wani babban mukami
Da duminsa: Shugaba Buhari ya nada AbdulMumini Jibrin wani babban mukami
Asali: Twitter

KU KARANTA: Idan aka hana kabilar Igbo shugabancin kasa a 2023, zamu hada kai da Nnamdi Kanu - Tsohon shugaban PDP

Haka kuma a jihar Kano, Kungiyar yan kasuwan man fetur masu zaman kansu IMAN, shiyar jihar , ta umurci mambobinta su fara sayar da man fetur a farashin N150 ga lita.

Daily Nigerian ta ce a jawabin da ya saki, shugaban kungiyar na jihar Kano, Bashir Dan-Mallam, ya ce umurnin ya biyo bayan sabon farashin sauyin farashin mai da kamfanin PPMC, mai hakkin sanya farashin mai.

A cewarsa, wannan mataki da suka zamu ya yi daidai da jawabin gwamnati cewa za ta rika canza farashin mai wata-wata dangane da yadda farashin ya canza a kasuwar duniya.

Dan Mallam ya hakaito jawabin PPMC inda ta ce an kara farashin kayan mai zuwa N138.62 ga lita a depot.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng