Ana wata ga wata: Yan kasuwa za su kara farashin litar mai zuwa N150

Ana wata ga wata: Yan kasuwa za su kara farashin litar mai zuwa N150

- Yan kasuwa na ci gaba da matsin lamva kan a kara kudin man fetur zuwa N150 akan kowacce lita daga watan Agusta

- Hakan ya biyo bayan karuwar farashin danyen mai a kasuwar mai ta duniya

- A watan da ya gabata ne hukumar PPRA ta sanar da karin kudin man fetur daga N140.80 zuwa N143.80 akan kowacce lita

Biyo bayan karuwar farashin danyen mai, 'yan kasuwa na ci gaba da matsin lamva kan a kara kudin man fetur zuwa N150 akan kowacce lita daga watan Agusta.

Hukumar da ke kayyade farashin man fetur ta kasa (PPRA) a watan da ya gabata ta sanar da karin kudin man daga N140.80 zuwa N143.80 akan kowacce lita.

Wannan shine karo na farko da hukumar ta amince da karin farashin man, tun bayan da aka cire tallafin man fetur a kasar.

Kafin daga farashin man a ranar 1 ga watan Yuli, a ranar 1 ga watan Yuli, hukumar ta amince da sayar da litar mai daga N121.50 zuwa N123.50.

KARANTA WANNAN: NDDC ta gayyaci Buhari ya bude wani babban aikinta da yaci N24bn a Bayelsa

Ana wata ga wata: Yan kasuwa za su kara farashin litar mai zuwa N150
Ana wata ga wata: Yan kasuwa za su kara farashin litar mai zuwa N150
Asali: Facebook

A wani labarin kuwa, wata majiya mai tushe ta shaidawa jaridar The Nation cewa 'yan kasuwa na yunkurin kara fashin man fetur sakamakon tashin farashin danyen mai a kasuwar duniya.

Gangar mai da ake sayarwa akan $43.24 a watan Yuli yanzu ta dawo ana sayar da ita akan $44.03.

Jaridar ta ruwaito cewa, "a yanzu ana cikin wani taro domin cimma matsaya ta sabon farashin da za a rinka sayar da man fetur daga watan Agusta.

"Yan kasuwa na bukatar PPRA da ta amince a sayar da man akan N150 kowacce lita daya saboda kudin danyen mai ya tashi kuma an janye tallafin mai a kasar."

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng