Sabbin mutum 288 sun kamu da cutar korona a Najeriya

Sabbin mutum 288 sun kamu da cutar korona a Najeriya

Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 288 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:44 na daren ranar Litinin 4 ga Augustan shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 288 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:

Sabbin mutum 288 sun kamu da cutar korona a Najeriya
Sabbin mutum 288 sun kamu da cutar korona a Najeriya
Asali: Facebook

Lagos-88

Kwara-33

Osun-27

FCT-25

Enugu-25

Abia-20

Kaduna-17

DUBA WANNAN: Jirgin sama makare da hodar-Iblis ya yi hatsari lokacin da ya ke kokarin tashi

Plateau-13

Rivers-13

Delta-10

Gombe-8

Ogun-4

Oyo-3

Katsina-1

Bauchi-1

Alkalluman da hukumar ta dakile cututtukan ta fitar a ranar Litinin 4 ga Augustan shekarar 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu da cutar ta korona a kasar 44,129 .

An sallami mutum 20,663 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 896.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel