Sabbin mutum 288 sun kamu da cutar korona a Najeriya

Sabbin mutum 288 sun kamu da cutar korona a Najeriya

Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 288 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:44 na daren ranar Litinin 4 ga Augustan shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 288 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:

Sabbin mutum 288 sun kamu da cutar korona a Najeriya
Sabbin mutum 288 sun kamu da cutar korona a Najeriya
Asali: Facebook

Lagos-88

Kwara-33

Osun-27

FCT-25

Enugu-25

Abia-20

Kaduna-17

DUBA WANNAN: Jirgin sama makare da hodar-Iblis ya yi hatsari lokacin da ya ke kokarin tashi

Plateau-13

Rivers-13

Delta-10

Gombe-8

Ogun-4

Oyo-3

Katsina-1

Bauchi-1

Alkalluman da hukumar ta dakile cututtukan ta fitar a ranar Litinin 4 ga Augustan shekarar 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu da cutar ta korona a kasar 44,129 .

An sallami mutum 20,663 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 896.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164