Masu cutar korona a Najeriya sun kai 43,841 - NCDC

Masu cutar korona a Najeriya sun kai 43,841 - NCDC

- A yanzu cutar korona ta bulla a duk jihohi 36 na Najeriya da kuma babban birnin kasar na Tarayya

- Jihar Legas ce ke jan ragama inda ta harbi mutum 15,267, mutum 2,160 suka warke sai kuma mutum 192 da suka riga mu gidan gaskiya

- A halin yanzu cutar ta harbi mutum 43,841, sai kuma mutum 20,308 da suka samu waraka, yayin da mutum 888 suka riga mu gidan gaskiya

Ya zuwa yanzu dai an samu bullar cutar korona a duk jihohi 36 na Najeriya da kuma birnin tarayya kamar yadda kididdigar hukumar dakile cututtuka masu yaduwa a kasar NCDC ta tabbatar.

Tabbas mahukuntan lafiya na ci gaba fadi-tashi ba dare ba rana domin dakile yaduwar cutar korona a Najeriya, sai dai fa lamarin ya ci tura domin kuwa cutar na ci gaba da bazuwa tamkar wutar daji.

Taskar bayanai ta NCDC a ranar Lahadi, 2 ga watan Agustan 2020, ta ce cutar korona ta harbi mutane 43,841 a duk fadin kasar.

Shugaban hukumar NCDC; Chikwe Ihekweazu
Shugaban hukumar NCDC; Chikwe Ihekweazu
Asali: Twitter

Haka kuma alkaluman sun nuna cewa an sallami mutum 20,308 daga cibiyoyin killace masu cutar bayan da suka warke.

Jadawalin NCDC ya tabbatar da cewa ya zuwa yanzu dai cutar korona ta hallaka mutum 888 a fadin kasar.

KARANTA KUMA: Ku kare kanku daga harin makiyaya da na 'yan daban daji - Kaigama ya shawarci 'yan Najeriya

Da misalin karfe 11.26 na ranar Lahadi da daddare, NCDC ta sanar da cewa an gano karin sabbin mutane 304 da cutar ta harba a fadin Najeriya.

Sabbin mutane 304 da cutar ta harba cikin jihohin 15 sun kasance kamar haka:

Legas (81), Abuja (39), Abia (31), Kaduna (24), Ribas (23), Filato (16), Cross River (13), Ebonyi (12), Ondo (12) Ekiti (11), Edo (11), Benuwe (10), Nasarawa (10), Ogun (6), Gombe (5)

Har ila yau jihar Legas ce a kan sahu na gaba ta fuskar yawan mutanen da cutar ta harba, sai kuma birnin Abuja a mataki na biyu yayin da jihar Oyo ta biyo bayansu a mataki na uku.

Legas - 15,267

Abuja - 3,972

Oyo - 2,768

Edo - 2,311

Rivers - 1,829

Kano - 1,597

Delta - 1,510

Kaduna - 1,481

Ogun - 1,403

Filato - 1,227

Ondo - 1,204

Enugu- 821

Ebonyi - 808

Kwara - 753

Katsina - 745

Borno - 613

Gombe - 612

Abia - 582

Bauchi - 560

Osun - 553

Imo - 469

Benue - 356

Nasarawa - 339

Bayelsa - 339

Jigawa - 322

Neja - 223

Akwa Ibom - 221

Adamawa - 164

Sokoto - 154

Ekiti - 152

Anambra - 135

Kebbi - 90

Zamfara - 77

Yobe - 67

Cross River - 58

Taraba - 54

Kogi - 5

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel