Abubuwa sun dagulewa Godwin Obaseki: Jerin mutane 42 da sukayi murabus daga gwamnatinsa

Abubuwa sun dagulewa Godwin Obaseki: Jerin mutane 42 da sukayi murabus daga gwamnatinsa

- Abubuwa na neman dagulewa gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki

- Ma'aikatansa da magoya bayansa na hannun riga da shi ana sauran yan makonni zaben gwamnan jihar

- Kawo yanzu mambobin kwamitin yakin neman zabensa akalla da abokan aikin sun yi murabus kuma sun koma bayan dan takaran APC

Abubuwa na neman rikicewa gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki, yayinda manyan ma'aikata da abokan aikinsa suke fita daga gwamnatinsa ana sauran yan makonnin zabe.

Gwamnan ya fara fuskantar wannan kalubale ne tun bayan lokacin da ya sauya sheka daga jam'iyyar All Progressives Congress APC zuwa jam'iyyar People Democratic Party PDP.

Sakamakon fitarsa, wasu mabiyansa irin tsohon kakakin majalisar dokokin jihar, Kabiru Adjoto, sun bi sahunsa.

Amma da alamun wadanda suka fita daga tafiyarsa sun fi adadin wadanda suka bisa.

Abubuwa sun dagulewa Godwin Obaseki: Jerin mutane 42 da suka murabus daga gwamnatinsa
Abubuwa sun dagulewa Godwin Obaseki: Jerin mutane 42 da suka murabus daga gwamnatinsa
Asali: UGC

Legit.ng Hausa ta tattaro muku jerin sunayen mutane 42 da sukayi murabus daga gwamnatin Obaseki:

1. John Mayaki - Sakataren yada labarai

2. Kehinde Garrick Osemwingie - sakataren Uhumwonde LGC

3. Taiwo Akerele - Shugaban ma'aikatar fadar gwamnatin jihar

4. Paul Ohonbamu - Kwamishana

5. Maureen Osaro Ekhoragbon - Mataimakin shugaban karamar hukumar Ovia North East

6. Omua Oni-Okpako - Kwamishana

7. Fulani Yakubu Ekpeyoung -SSA

8. Hon. Adeyanju Noah - SSA

9. Madam Cordelia M. Iyogun - SSA

10. James Osheku - SSA

11.Louis Osamuyi Osayande - SSA

12. Ernest Unuaghon imina - SSA

13. Goodluck A. Uyigue - SA

14. Hon. Razaq Rotimi - SA

15. Olajide Victor Oloruyomi - SA

16. Smart Bank - SA

17. Chris Oseiwe Oribhabor - SSA

18. Comr. Solomon Okoduwa - SSA

19. Kennedy Itepu - SSA

20. Sabbath Egbeyon - SSA

21. Osamwonyi Atu - EDSOGPADEC

22. Emmanuel Odigie - EDSOGPADEC

23. Aiwanu Oshiomhole - EDSOGPADEC

24. Okondoh Patrick Iyoha - OSM State director

25. Gabriel Oiboh - Shugaban hukumar makarantun sakandare

26. Bright Njor - SA

27. Kingsley Ekueme - SA

28. Joshua Akhabue - SA

29. Oladele Ayotope Josiah - SA

30. Boyi Magdalene - SA

31. Osarobo Osaro Anthony - SA

32. Aibangbee Chico - SA

33. Obayagbona Augustine - SA

34. Otaniyen Igbinosa - Orhiomwon supervisor

35. Martins Ozakpolor - Orhiomwon supervisor

36. Vincent Ehibor - Orhiomwon supervisor

37. Christopher Adesotu - Shugaban hukumar ilmin aikin hannu

38. Festus Ese Omoruyi SA -

39. Aghedo Oscar - Sakatare Ovia North East

40. Emike Obazee - SA

41. Monday Ogiegor - MD EDSTMA

42. Prince Lucky Igbinedion - SSA

A bangare guda, tsohon gwamnan jihar Edo kuma tsohon shugaban jam'iyyar APC, Adams Oshiomole, ya tabbatarwa mabiya jam'iyyar cewa zasu samu gagarumin nasara a zaben bana.

Za'a gudanar da zaben ne ranar Asaba, 19 ga watan Satumba, 2020.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel