Cikin mako daya, an kashe mutane 142, an yi garkuwa da 44 a Arewacin Najeriya

Cikin mako daya, an kashe mutane 142, an yi garkuwa da 44 a Arewacin Najeriya

Akalla mutane 142 aka kashe a hare-hare daban-daban a Arewacin Najeriya cikin mako daya (18 ga Yuli zuwa 24 ga Yuli), wani rahoton da Premium Times ta samu ya nuna.

Hakazalika an yi garkuwa da mutane akalla 44 a Arewa yayinda matsalan rashin tsaro ke cigaba munana a fadin tarayya.

A cewar rahoton cibiyar harkokin waje CFR, adadin wadanda suka mutu sun fi yawa a jihar Kaduna sakamakon hare-hare shida da akai, sannan jihar Katsina, mahaifar shugaba Muhammadu Buhari, inda aka kai hare-hare hudu.

Cibiyar ta kasar Amurka, ta ce tana bibiyan matsalan rashin tsaro a fadin Najeriya "ta hanyar amfani da labaran da aka wallafa a jaridu, kuma daga iyalan wadanda aka kaiwa hare-hare."

Cikin mako daya, an kashe mutane 142, an yi garkuwa da 44 a Arewacin Najeriya
Cikin mako daya, an kashe mutane 142, an yi garkuwa da 44 a Arewacin Najeriya
Asali: Facebook

KU KARANTA: Na fi karfin inyi fada a Dogara, ya yi kadan - Gwamnan Bauchi, Bala Mohammed

Filla-filla:

A bayanan filla-filla, rahoton ya bayyana cewa a ranar 23 ga Yuli, wasu makiyaya sun hallaka mutane bakwai a Kajuru, jihar Kaduna kuma washe gari ranar 24 ga Yuli, yan bindiga sun hallaka mutane 10 a karamar hukumar Jema'a da Kaduna, duk a jihar Kaduna.

A ranar 18 ga Yuli, an yi garkuwa da mutane shida a Chikun, jihar Kaduna, yayinda ake zargin makiyaya da kisa mutane 11 a Zangon Kataf ranar 20 ga Yuli.

Rahoton ya kara da cewa a ranar 19 ga Yuli, wasu makiyaya sun hallaka mutane 21 da wani dan sanda a Kaura, yayinda rikici kabilanci yayi sanadiyar mutuwar mutane uku a Kauru, jihar Kaduna ranar 21 ga Yuli.

A cewar rahoton CFR, bam ya hallaka yara shiga a Malumfashi, jihar Katsina ranar 18 ga Yuli, yayinda aka hallaka Sojoji 23 da yan bindiga 17 a Jibia, jihar Katsina.

Washe gari ranar 21 ga Yuli, yan bindiga sun hallaka mutane uku a Batsari yayinda aka sace mutane 17 a Safana ranar 22 ga Yuli a jihar Katsina.

A cewar rahoton, yan Boko Haram sun kashe ma'aikatan kungiyoyin agaji biyar a ranar 22. Kuma a ranar sun hallaka mutane uku a garin Chibok.

A ranar 20 ga Yuli, harin jirgin saman Soji yayi sanadiyar mutuwar akalla yan bindiga 10 a Talata-Mafara, jihar Zamfara, yayinda aka sake hallaka yan bindiga 10 a hanyar Birnin Magaji/Kiyawa na jihar ranar 23 ga Yuli.

A jihar Tarana ranar 19 ga Yuli, masu garkuwa da mutane sun kashe mutane biyu da suka sace yayinda jami'an tsaro suka hallaka masu garkuwa hudu a hanyar Lokoja, jihar Kogi a ranar.

Rahoton ya karashe cewa a ranar 19 ga Yuli, an yi garkuwa da mutane 16 a Rafi, jihar Neja, yayinda akayi garkuwa da mutane 5 a Jada, jihar Adamawa.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng