Babu sauran mai Korona a jihar Sokoto, Zamfara da Kogi

Babu sauran mai Korona a jihar Sokoto, Zamfara da Kogi

Alkaluma daga hukumar hana yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC sun nuna cewa jihohi uku a Najeriya sun waye gari babu sauran masu cutar Korona cikinsu.

Wadannan jihohin sun hada da Sokoto, Zamfara da Kogi.

A jihar Zamfara, mutane 76 ne suka kamu da cutar tun lokacin da ta bulla, yayinda 71 suka samu waraka kuma aka sallamesu, mutane 5 sun mutu sakamakon haka.

Sama da makonni hudu kenan ba'a samu sabon mai cutar ba. Jihar Zamfara ce jiha daya da ta dade ba'a kara samun mai cutar ba.

A bangaren jihar Sokoto, mutane 153 ne suka kamu da cutar tun lokacin da ta bulla, yayinda 137 suka samu waraka kuma aka sallamesu, mutane 16 sun mutu sakamakon haka.

A jihar Kogi kuwa, mutane 5 ne suka kamu da cutar tun lokacin da ta bulla, yayinda 3 suka samu waraka kuma aka sallamesu, mutane 2 sun mutu sakamakon haka.

Hukumar NCDC na kuka da rashin bada hadin kai ta bangaren gwamnatin jihar Kogi.

Hukumar hana yaduwar cututtuka a Najeriya (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 595 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:53 na daren ranar Alhamis 16 ga Yulin shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 595 da suka fito daga jihohin Najeriya.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng