Buhari ya jagoranci zaman majalisar zartarwa a fadar shugaban kasa

Buhari ya jagoranci zaman majalisar zartarwa a fadar shugaban kasa

- Buhari ya jagoranci zaman majalisar zantarwa karo na shida ana kiyaye dokar nesa-nesa da juna

- Ministoci 11 sun halarci zaman majalisar da shugaba Buhari ya jagoranta a yau Laraba, 8 ga watan Yuli

- Yayin zaman majalisar, an yi alhinin mutuwar tsohon ministan wasanni da matasa, Alhaji Inuwa Abdulqadir

A yau Laraba, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranci zaman majalisar zartarwa a fadar gwamnatinsa ta Aso Villa da ke babban birnin Tarayya Abuja.

Wannan shi zaman majalisar na shida da shugaban kasar ya jagoranta da aka kiyaye dokar nesa-nesa da juna inda ta hanyar amfani da yanar gizo wajen tattaunawa.

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa, ministocin da a dole su na da ta cewa kuma su na dauke da bayanan da za su gabatar su ne kadai suka halarci zaman majalisar a fadar shugaban kasa.

Zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba, 8 ga watan Yulin 2020
Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Nation
Zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba, 8 ga watan Yulin 2020 Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Nation
Asali: Twitter

Zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba, 8 ga watan Yulin 2020
Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Nation
Zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba, 8 ga watan Yulin 2020 Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Nation
Asali: Twitter

Zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba, 8 ga watan Yulin 2020
Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Nation
Zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba, 8 ga watan Yulin 2020 Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Nation
Asali: Twitter

Zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba, 8 ga watan Yulin 2020
Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Nation
Zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba, 8 ga watan Yulin 2020 Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Nation
Asali: Twitter

Kusoshin gwamnatin da suka halarci zaman a wannan mako sun hadar da mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo; Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha; da shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, Ibrahim Gambari.

Ministoci 11 ne suka halarci zaman ciki har da;

Ministan kasafi da tsare-tsaren - Zainab Ahmed

Ministan Sufuri - Honarabul Rotimi Amaechi

Ministan Labarai da Al'adu - Alhaji Lai Mohammed

Ministan Ayyuka da Gidaje - Mista Babatunde Fashola

Ministan Sufurin Jiragen Sama - Sanata Hadi Sirika

Ministan Shari'a Kuma Lauyan Koli na Kasa - Abubakar Malami

Ministan Harkokin Neja Delta - Godswill Akpabio

Ministan Harkokin Waje - Geoffery Onyeama

Ministan Ayyuka na Musamman - George Akume

Ministan Ilimi - Adamu Adamu

Karamin Ministan Harkokin Waje - Ambasada Zubairu Dada.

KARANTA KUMA: WAEC ta shata sharudan zana jarrabawar bana

Gabanin fara tattaunawa kan al'amuran da suka shafi zaman majalisar na yau, shugaba Buhari ya nemi da a yi shiru na minti daya domin yin alhinin mutuwar tsohon ministan wasanni da matasa; Inuwa Abdulqadir.

Marigayi Inuwa yan daya daga cikin mambobin tsohon kwamitin gudanarwa kuma tsohon shugaban jam'iyyar APC na kasa reshen Arewa mao Yamma, wanda ajali ya katse masa hanzari a ranar Litinin.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel