Buhari ya jagoranci zaman majalisar zartarwa a fadar shugaban kasa

Buhari ya jagoranci zaman majalisar zartarwa a fadar shugaban kasa

- Buhari ya jagoranci zaman majalisar zantarwa karo na shida ana kiyaye dokar nesa-nesa da juna

- Ministoci 11 sun halarci zaman majalisar da shugaba Buhari ya jagoranta a yau Laraba, 8 ga watan Yuli

- Yayin zaman majalisar, an yi alhinin mutuwar tsohon ministan wasanni da matasa, Alhaji Inuwa Abdulqadir

A yau Laraba, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranci zaman majalisar zartarwa a fadar gwamnatinsa ta Aso Villa da ke babban birnin Tarayya Abuja.

Wannan shi zaman majalisar na shida da shugaban kasar ya jagoranta da aka kiyaye dokar nesa-nesa da juna inda ta hanyar amfani da yanar gizo wajen tattaunawa.

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa, ministocin da a dole su na da ta cewa kuma su na dauke da bayanan da za su gabatar su ne kadai suka halarci zaman majalisar a fadar shugaban kasa.

Zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba, 8 ga watan Yulin 2020
Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Nation
Zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba, 8 ga watan Yulin 2020 Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Nation
Asali: Twitter

Zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba, 8 ga watan Yulin 2020
Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Nation
Zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba, 8 ga watan Yulin 2020 Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Nation
Asali: Twitter

Zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba, 8 ga watan Yulin 2020
Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Nation
Zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba, 8 ga watan Yulin 2020 Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Nation
Asali: Twitter

Zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba, 8 ga watan Yulin 2020
Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Nation
Zaman majalisar zartarwa na ranar Laraba, 8 ga watan Yulin 2020 Hakkin mallakar hoto; Jaridar The Nation
Asali: Twitter

Kusoshin gwamnatin da suka halarci zaman a wannan mako sun hadar da mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo; Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha; da shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, Ibrahim Gambari.

Ministoci 11 ne suka halarci zaman ciki har da;

Ministan kasafi da tsare-tsaren - Zainab Ahmed

Ministan Sufuri - Honarabul Rotimi Amaechi

Ministan Labarai da Al'adu - Alhaji Lai Mohammed

Ministan Ayyuka da Gidaje - Mista Babatunde Fashola

Ministan Sufurin Jiragen Sama - Sanata Hadi Sirika

Ministan Shari'a Kuma Lauyan Koli na Kasa - Abubakar Malami

Ministan Harkokin Neja Delta - Godswill Akpabio

Ministan Harkokin Waje - Geoffery Onyeama

Ministan Ayyuka na Musamman - George Akume

Ministan Ilimi - Adamu Adamu

Karamin Ministan Harkokin Waje - Ambasada Zubairu Dada.

KARANTA KUMA: WAEC ta shata sharudan zana jarrabawar bana

Gabanin fara tattaunawa kan al'amuran da suka shafi zaman majalisar na yau, shugaba Buhari ya nemi da a yi shiru na minti daya domin yin alhinin mutuwar tsohon ministan wasanni da matasa; Inuwa Abdulqadir.

Marigayi Inuwa yan daya daga cikin mambobin tsohon kwamitin gudanarwa kuma tsohon shugaban jam'iyyar APC na kasa reshen Arewa mao Yamma, wanda ajali ya katse masa hanzari a ranar Litinin.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng