Zaben Gwamnan Ondo: PDP ta zabi Matawalle ya jagoranci kwamitin yakin neman zabe

Zaben Gwamnan Ondo: PDP ta zabi Matawalle ya jagoranci kwamitin yakin neman zabe

Kwamitin gudanarwa na jam'iyyar PDP na kasa, ya amince da nadin Gwamna Muhammadu Bello Matawalle na jihar Zamfara, a matsayin wanda zai jagoranci kwamitin yakin neman zaben gwamnan jihar Ondo.

Babban sakatare a kwamitin gudanarwa na jam'iyyar, Austin Akobundu, shi ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin cikin birnin Abuja.

Mista Akobundu ya ce, kwamitin ya kuma amince da nadin Cynthia Egwa, David Vaughan da Ginger Onwusibe a matsayin mambobin kwamitin da Gwamna Matawalle zai jagoranta.

Kamar yadda jaridar Daily Nigerian ta ruwaito, kwamitin ya kuma amince da Kingsley Chinda a matsayin sakatare.

Gwamna Muhammad Bello Matawalle na jihar Zamfara
Gwamna Muhammad Bello Matawalle na jihar Zamfara
Asali: Twitter

Ya ce an ratayawa kwamitin nauyin zaben wakilan zabe uku a kowane daya daga cikin mazabu 203 da ke fadin jihar.

An shirya fara wannan aiki ne a ranar Laraba, 8 ga watan Yuli a duk fadin jihar.

Tun tsawon watanni da suka gabata, hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta INEC, ta sanya ranar 10 ga watan Oktoba a matsayin ranar da za a gudanar da zaben gwamnan Ondo.

Legit.ng ta kuma ruwaito cewa, kwamitin gudanarwa na jam'iyyar PDP, a ranar Juma'ar da ta gabata, ya nada gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike a matsayin shugaban kwamitin yakin neman zaben gwamnan jihar Edo.

KARANTA KUMA: Gwamnatin Tarayya ta bai wa jihohi umarnin bude makarantu

Jam'iyyar ta sanar da hakan ne a kan shafinta na Twitter, inda ta bayyana gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri, a matsayin mataimakin kwamitin yakin neman zaben.

Wannan lamari ya faru ne kwana daya bayan da jam'iyyar APC ta nada gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, a matsayin shugaban kwamitin yakin neman zaben gwamnan jihar ta Edo.

A ranar Asabar, 19 ga watan Satumba na 2020, za a gudanar da zaben gwamna a jihar Edo, inda gwamna mai ci Godwin Obaseki, zai gwabza da dan takara na jam'iyyar APC; Osagie Ize-Iyamu.

Makonni kadan da suka gabata ne Gwamna Godwin Obaseki dai ya sauya sheka daga APC ya koma PDP kuma jam'iyyar ta tsayar da shi takara ba tare da wata-wata ba.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng