Jerin gwamnoni 7 da suka kamu da cutar Coronavirus, 4 sun warke (Hotuna)
Bayan watanni hudu da bullar cutar Coronavirus a Najeriya, Akalla gwamnoni 7 sun kamu da cutar.
Adadin wadanda suka kamu da cutar kawo yammacin Juma'a sun kai 27,564 bisa alkaluman hukumar hana yaduwar cututtuka a Najeriya wato NCDC.
Cutar ta yadu cikin mutane daban-daban wanda ya hada da yan siyasa, malaman addini, manyan yan kasuwa, Likitoci, Malaman jinya, da sauran su.
Ga jerin gwamnonin bakwai da Korona ta harba.
1. BALA MOHAMMED: Ya kwashe kwanaki 15 a killace
Gwamnan jihar Bauchi, Bala AbdulKadir Mohammed, ne gwamnan farko da ya kamu da cutar COVID-19.
A ranar 24 ga Maris, hadiminsa, Mukhtar Gidado, ya saki jawabin cewa gwamnan ya killace kansa. Amma ranar 9 ga Afrilu gwamna ya warke.
2. NASIR EL-RUFAI: Ya kwashe makonni 3 a killace
Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i ne gwamna na biyu da cutar a Najeriya. Hakazalika shine mutumin farko da ya kamu da cutar a jiharsa.
A faifan bidiyon da ya saki ranar 28 ga Maris, gwamnan ya sanar hakan.
3. SEYI MAKINDE: Ya warke cikin kasa da mako daya
A ranar 30 ga Maris, gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, ya sanar da cewa ya killace kansa bayan kamuwa da cutar Coronavirus.
4. IKEAZU IKPEAZU: Ya warke bayan kimanin wata daya
Gwamnan jihar Abia, Ikpeazu ya sanar da cewa ya kamu da cutar ranar 8 ga Yuni, 2020.
Bayan kimanin wata daya, gwamnan ya warke ranar Asabar, 4 ga watan Yuli.
5. IFEANYI OKOWA
Gwamnan jihar Delta, Ifeanyi Okowa ya kamu da cutar Corona tare da matarsa, Edith, da daya cikin 'yayansa mata.
Har yanzu suna jinya
6. ROTIMI AKEREDOLU
A ranar Talata, gwamnan jihar Ondo, ya sanar da cewa ya kamu da cutar COVID-19. Amma Akeredolu ya bayyana cewa duk da cewa yana killace, ba zai mika ragamar mulki hannun mataimakinsa ba.
Har yanzu yana jinya
7. David Umahi
Gwamnan jihar Ebonyi, Dave Umahi, ne gwamnan karshe da ya kamu yanzu. Ya sanar da kamuwarsa da cutar ne a yau Asabar.
Hakazalika ya sanar da cewa ya wasu daga cikin hadimansa sun kamu da cutar.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng