Yanzu-yanzu: Gobara ta tashi a ofishin CBN dake jihar Gombe

Yanzu-yanzu: Gobara ta tashi a ofishin CBN dake jihar Gombe

Goabara ta tashi a babbar bankin Najeriya dake jihar Gombe ranar Juma'a, 3 ga watan Yuli, 2020.

Sahara Reporters ta sami rahoto daga majiya cewa gobarar ta fara ci ne misalin karfe 10 na safe.

Wannan ya shiga jerin gobara da aka samu a ma'aikatun gwamnati a fadin tarayya cikin yan watannin nan.

Yanzu-yanzu: Gobara ta tashi a ofishin CBN dake jihar Gombe
Yanzu-yanzu: Gobara ta tashi a ofishin CBN dake jihar Gombe
Asali: Original

A baya Legit.ng Hausa ta kawo muku jerin ofishoshin gwamnati biyar da suka zalzala cikin wata daya.

1. Ofishin akawunta janar (Gidan baitul mali)

A ranar 8 ga Afrilu, 2020, Ginin da aka fi sani da 'Gidan baitul mali' wato Treasury House' na kusa da hedkwatar hukumar yan sandan Abuja, a unguwar Garki ya yi gobara.

2. Hedkwatar hukumar CAC

A ranar 15 ga Afrilu, Gobara ta tashi a hedikwatar hukumar yi wa kasuwanci rijista ta kasa (CAC) da ke unguwar Maitama a birnin tarayya, Abuja.

Gobarar ta babbake hawa na karshe a ginin ofishin hukumar CAC mai bene hawa bakwai, tare da lalata muhimman kayayyaki.

3. Hedkwatar INEC dake Abuja

A ranar 17 ga watan Afrilu, Hedkwatar hukumar gudanar da zabe ta kasa watau INEC dake birnin tarayya Abuja ya ci da wuta.

4. Ofishin babban bankin Najeriya CBN

A ranar 21 ga Afrilu, an samu gobara a ofishin babban bankin Najeriya CBN, reshen Jos, jihar Plateau. Bankin ta tabbatar da hakan a shafinta na Tuwita inda ta bayyana cewa tuni an kashe wutar.

5. Hedkwatar NIPOST

A ranar 20 ga watan Mayu, 2020, Mumunar gobara ya auku a hedkwatar hukumar ayyukan aika da karban sako watau NIPOST dake birnin tarayya Abuja.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng