Yanzu-yanzu: PPPRA ta bayar da shawarar kara kudin litar man fetur zuwa N140

Yanzu-yanzu: PPPRA ta bayar da shawarar kara kudin litar man fetur zuwa N140

Hukumar Kula Da Farashin Albarkatun Man Fetur (PPPRA) ta bayar da shawarar a kara farashin litar man fetur daga farashin daga N121.50 da ake siyar wa a baya.

A cewar hukumar, sabon farashin da ya dace a rika sayar wa shine tsakanin N140.80 zuwa N143.80 duk lita kamar yadda The Cable ta ruwaito.

Yanzu-yanzu: PPPRA ta bayar da shawarar kara kudin litar man fetur zuwa N140
Yanzu-yanzu: PPPRA ta bayar da shawarar kara kudin litar man fetur zuwa N140. Hoto daga Factprint
Asali: UGC

DUBA WANNAN: Fitattun 'yan Najeriya 12 da suka rasu a watan Yuni

Hukumar ta PPPRA cikin wani takarda da ta fitar a ranar 1 ga watan Yulin 2020 ga dillalan man fetur ta ce;

"Bayan yin nazari a kan yadda yanayin kasuwa ta kasance a watan Yuni da yadda yan kasuwa ke sayan man fetur, muna bayar da shawarar sabon farashin litar man fetur a watan Yulin 2020 ya kasance daga N140.80-N143.80 duk lita.

"Ana shawartar dukkan yan kasuwa su rika sayar da hajojinsu a farashin da PPPRA ta bayar da shawarar a sayar."

Hukumar a ranar 31 ga watan Mayun 2020 ta bayar da shawarar a rika sayar da litar man fetur tsakanin N121.50 to N123.50.

Wannan na nuna akwai yiwuwar farashin litar na man fetur ya sauya a karshen watan Yuli bisa laakari da yadda kasuwa ta kasance.

Wata majiya daga hedkwatan hukumar da ke Abuja ta ce karin farashin danyen mai a kasuwanin duniya ne ya janyo karin farashin litar man fetur din kamar yadda The Punch ta ruwaito.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164