Yanzu-yanzu: Sabbin mutum 490 sun kamu da cutar Korona a Najeriya

Yanzu-yanzu: Sabbin mutum 490 sun kamu da cutar Korona a Najeriya

Hukumar Dakile Cututtuka Masu Yaduwa ta Najeriya (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 490 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11.28 na daren ranar Lahadi 28 ga Yunin shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 490 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

Yanzu-yanzu: Sabbin mutum 490 sun kamu da cutar Korona a Najeriya
Yanzu-yanzu: Sabbin mutum 490 sun kamu da cutar Korona a Najeriya
Asali: Twitter

Lagos-118

Delta-84

Ebonyi-68

FCT-56

Plateau-39

Edo-29

Katsina-21

Imo-13

Ondo-12

Adamawa-11

DUBA WANNAN: Bidiyon wani mutum da mace suna lalata a kan titi cikin motar UN ya jawo cece-kuce

Osun-8

Ogun-8

Rivers-6

Kano-5

Enugu-3

Bauchi-3

Akwa Ibom-3

Kogi-1

Oyo-1

Bayelsa-1

Alkalluman da hukumar ta dakile cututtukan ta fitar a ranar Lahadi 28 ga Yunin shekarar 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu da cutar ta korona a kasar 25,567.

An sallami mutum 9007 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 565.

A wani labarin, kun ji cewa an birne gawar tsohon gwamnan jihar Oyo, Sanata Abiola Ajimobi a ranar Lahadi a garin Ibadan babban birnin jihar Oyo.

An yi wa Ajimobi jana'iza irin ta koyarwar addinin musulunci sannan aka birne shi a gidansa da ke 6th Avenue, Yemoja Street, Oluyole Estate, Ibadan cikin yanayi na tsaro kamar yadda The Punch ta ruwaito.

Gwamnatin jihar ta Oyo ta ki amincewa a birne marigayin a gidansa da ke Agodi GRA saboda ana shariar a kotu game da gidan duk da cewa nan iyalansa suka fi so.

An birne tsohon shugaban riko na jami'yyar All Progressives Congress, APC, mai mulki misalin karfe 10:05 na safe.

Ajimobi, mai shekaru 7 a duniya ya rasu ne a wani asibiti da ke Legas.

Rahotanni sun ce an bi dukkan dokokin birne wadanda suka mutu sakamakon cutar coronavirus yayin janai'zarsa.

Mutanen da suka hallarci jana'izar ba su kai 2 ba cikinsu har da matar tsohon gwamnan, Cif Florence Ajimobi da wasu daga cikin iyalansa na yan uwansa na kusa.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164