Hotunan yadda aka binne gawar Ajimobi a gidansa da ke Ibadan

Hotunan yadda aka binne gawar Ajimobi a gidansa da ke Ibadan

An birne gawar tsohon gwamnan jihar Oyo, Sanata Abiola Ajimobi a ranar Lahadi a garin Ibadan babban birnin jihar Oyo.

An yi wa Ajimobi jana'iza irin ta koyarwar addinin musulunci sannan aka birne shi a gidansa da ke 6th Avenue, Yemoja Street, Oluyole Estate, Ibadan cikin yanayi na tsaro kamar yadda The Punch ta ruwaito.

Gwamnatin jihar ta Oyo ta ki amincewa a birne marigayin a gidansa da ke Agodi GRA saboda ana shariar a kotu game da gidan duk da cewa nan iyalansa suka fi so.

Yanzu-yanzu: An birne Ajimobi a gidansa da ke Ibadan
Yanzu-yanzu: An birne Ajimobi a gidansa da ke Ibadan. Hoto daga Oyo Insight
Asali: UGC

Yanzu-yanzu: An birne Ajimobi a gidansa da ke Ibadan
Yanzu-yanzu: An birne Ajimobi a gidansa da ke Ibadan. Hoto daga Oyo Insight
Asali: UGC

DUBA WANNAN: Bidiyon lalata: UN ta fara bincike a kan wandanda suka yi latata a motarta

An birne tsohon shugaban riko na jami'yyar All Progressives Congress, APC, mai mulki misalin karfe 10:05 na safe.

Ajimobi, mai shekaru 7 a duniya ya rasu ne a wani asibiti da ke Legas.

Yanzu-yanzu: An birne Ajimobi a gidansa da ke Ibadan
Yanzu-yanzu: An birne Ajimobi a gidansa da ke Ibadan. Hoto daga Oyo Insight
Asali: UGC

Yanzu-yanzu: An birne Ajimobi a gidansa da ke Ibadan
Yanzu-yanzu: An birne Ajimobi a gidansa da ke Ibadan. |Hoto daga Oyo Insight
Asali: UGC

Rahotanni sun ce an bi dukkan dokokin birne wadanda suka mutu sakamakon cutar coronavirus yayin janai'zarsa.

Mutanen da suka hallarci jana'izar ba su kai 2 ba cikinsu har da matar tsohon gwamnan, Cif Florence Ajimobi da wasu daga cikin iyalansa da yan uwansa na kusa.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164